ane sha'ani batare da gajiyawa ba".
Jikinta yayi sanyi tabbas ta gaddame masa yana dab da zargin
wani abu, don haka sai ta karkace ta gyara zamanta ta kalle shi “Idan
dama taki sai koma hagu maganarka gaskiya ce, fatanmu ka kasance
cikin karsashi kamar koda yaushe?"
Tana fadin haka yayi shiru idanuwansa na kallon guri guda,
gaba daya hankalinta ya bar wajen jira take yi kawai Zulehat ko
Hauletu su karaso cikin lambu ta mike dan zuwa ta sa a yi mata kiran
Mustafa ta kuma gana da waziri.
'Yarsa ce Gimbiya Zahra, ta nufo lambon cikin ado barori
biyu na taki mata baya, tsawon nisan tafiya taku gomasha biyu da
inda Sarki yake barorin suka tsaya gami da sunkuyar da kawunansu
kar, don kada su kalli inda Sarki yake, daga nan ne Gimbiya Zahra ta
ci gaba da tafiya har ta iso wajen da ake tanadarwa mahaifinta dan
hutuwa da yammaci sakaliya. Gimbiya Zahra ta sunkuyar da kai kasa
ta yi gaisuwa ga mahaifinta, ya amsa mata cikin murmushi da nuna
mata waje kusa da shi ya ce "Zo ki zauna”.
bature
86 Page
Ta tafi cikin ladabi ta samu wajen zama ta zauna daf da ashi
ya dafa bayan "Ya Zahra ta, kyakkyawar diya ta, mene ne
damuwarki?"
Ta yi murmushi ta kalli Sarauniya Siyama dake a takure waje
guda duk hankalinta ya dagule ta rasa mene ne abin da zata yi don
magance matsalar da za a jefa su ciki.
Ta tuna wasu lokutan can baya a lokacin da Likitan Sarki
Mustafa ya fito daga sashin sarki yana kokarin duk damuwa ta dame
shi adai-dai lokaci Siyama ta biyo bayansa bayan ta fuskanci ya
fahimci abin da yake damun Sarki yaki yin Magana ne saboda bai
san yadda maganar zata zama a cikin gidan ka iya yiwuwa ya yi laifin da zai ja masa kisa, ko wani dauren saboda babu wani likita
amintacce da Sarki ya yadda da shi kamar Mustafa. ta yi sauri ta sha
gabansa a lokacin da ta lura da babu mai ganinsu, su ka yi ido biyu gege domin da Mustafa. Mustafa yana muzurai yana kallon gefe da
kadaice da matan Sarki matukar ba dakin gani ba haramun ne kuma
kisa ne a kanka saboda hakan sai hankalinsa ya tashi.
"Kwantar da hankalinka babu wani da zai gan mu”.
Ya dube ta da alamun tambaya ta riga shi kara wata maganar
"Akwai wani abu dangane da ciwon Sarki me yake faruwa?"
Ya fara nuku-nuku ta daka masa tsawa "Ka fada min me ka
fuskanta?"
Babu yadda zai yi yace "Aikin sihiri ne, da aka yi amfani da
shi a bargon da karkashin matashin kansa tsawon lokaci su ne suka
haifar masa da ciwonsa, daga kwakwala zuwa karfin jiki, sihiri ne
mai karfe da ya kashe masa karfin jiki ya kuma kashe masa karfin ^
nazari da hangen nesa".
R
Ta dube shi tana nazarinsa domin tana da sakon da zata bashi
"Me kake tunanin aikatawa yanzu ina nufin me za a yiwa Sarki da
zai samu lafiya”.
bature
87 Page
"Ina son sanar da likita kuma sirikinsa bin Abbas ne domin
shi ne likita mafi rinjaye kuma yana aikin sihiri don haka shi ne
kadai zai iya da wannan al'amari da izinin Allah".
"Ibn Abbas, to ahir, ka da ka kuskura ka kawo wani cikin
gidan nan domin kula da Mai martaba kai ne za ka ci gaba da kulawa
da shi".
Ya dubeta yana son yi mata cikakken bayani bayan ya hadiye
wani yawo ya ce “Bani da kwarewar da zan iya magance matsaalar
Sarki ranki ya dade, matukar ana son Sarki ya samu lafiya dole ne sai
mun yi amfani da jarraba malamai wadanda suke da ilimi wajen
yakar sihiri, wannan yana ci masa jiki zuciya da kwakwalwa za ta iya
kai Sarki ya rasa hankalinsa wata rana ko kuma ya karfin lakar
jikinsa ta daina amfani, hakan zai iya sawa a rasa Sarki".
Ta Harare shi "Matukar ka sanar da wani wannan al'amari
abin da kake tsoro shi zai faru gare ka, domin zan maka sharrin kai
ne ka hadawa Sarki wannan sihirin idan kuma ka hakura ka ci gaba
da bashi taimako zan saka maka da mafificin alkairi ko bayan babu
rayuwar Sarki z aka ci gaba da kulawa da na Yarima Yazid.
Cikin rudani da tashin
dade?"
hakali ya ce "Me kike nufi ranki ya
"Ba sauri nake yi ba, na baka lokacin yin nazari da tunani,
sakamakon bijirewa za a dauki rayuwarka kacokan daga duk ranar da
ka yi tunanin sanarwa wani, duk sahun da zaka taka mutanenmu na
bibiyar lamarinka dan haka tunaninka da yankewa hukuncinka a
hannunmu yake"
Tana fadin haka ta nuna masa hanya domin ya ci gaba da
tafiya, sannu a hankali da sanyin jiki ya bar wajen..
Ta dawo daga wannan tunanin da ta yi hakan ya sa ta yi
karfinhali mikewa domin fita daga lambon Sarki. “Ranka ya dade,
bari na barka ‘yarka”.
bature
88 | Page
Batare da yayi mata Magana kai kawai ya jinjina mata ta mike ta fita barorinta na bakin hanya suka bi bayanta don mata
rakiya cikin gida.
"Baba tun da ka zama babu lafiya horar dani a matsayin
jaruma ya tsaya, babu mai kula ni ko Yaya Yazid ko Abbas". “Uhmm shine damuwar, rabu da su kin ji farin cikin idanuwana, zan samo likita ingantacce domin kulamin da lafiyata, ko don na ci gaba da baki horo, ai na gaya miki za mu tafi yaki tare kina bisa doki da takobi a hannunki kina wulwalata sama kina cire kan
munafukan Allah ta Allah'
"Da gaske Baba?"
"Sosai"