a fara
shawartarsa a game da wani abu dangane da gimbiya Suhaila bin
Ababakari, amma bangaren zuciya mara karfin gwiwa na bashi
labarin matsayinta da na sa matsayin wannan tunanin ya dawo masa
da mafarkin da yake kokarin dorawa ransa.
"Dan uwana rabin raina”.
Muryar Hamdiya ya karade kunnuwansu kuma ya dawo dasu
cikin hayyacinsu, cikin rashin gaskiyar da gimbiya take ciki na
tunani dole Hamdiya ta fuskanci abin da ke wakana don haka ta yi
sim-sim ta bar wajen. Ya dubi Hamdiya, da take kokari yi masa
Magana "Ban san me yasa kake son ka bada rayuwarka ga mutunen
da basu da amfani a gare k aba, dan uwa na sha kukan rashinka".
bature
82 Page
83 Page
Ya dube ta duba na mamaki "Ban fahimta ba,su waye basu da
marasa amfani a rayuwata?"
Ta juya ta dubi Gimbya da takekokarin shiga cikin gida shi
maya kalle ta tare da suka dawo da dubansu ga juna ya riga ta
Magana ya san abin da take son sanar da shi “Kin ga Hamdiya
rayuwarta ta kowane dan adamce matukar ya bada gaskiya ga
ubangijin talikai, babu wani dan adam da za a zalunta ina kallo
batare da na taimakeshi ba, ina so ki koyi hana kanki shiga cikin
lamurana, ki zauna a matsayinki na 'yar uwata, ki koya wa ranki
sanin cewa ban taba fita daga gida da saka san cewa lallai zan dawo
na same ku ba, saboda haka ban saka ki lalubamin mutanen da suke
da muhimmanci ko wadanda basu da shi a cikin lamurana".
Yana fadin haka ya bar wajen ya bata waje tana kallonsa
kamar ta fasa ihu don takaici.
**
Sarki Muhammad farsi Farsi shugaban kafatanin nahiyar
larabawa a zamaninsa, yana zaune cikin kulawar matarsa Siyama
tana shayar da shi kayan alatu a kyakkyawan lambon gidansa suna
taba hira sama sama, ta lura da akwai tarin damuwa ga Mijinta
Muhammad Farsi, don haka sai ta fara tunanin ta yadda za ta shawo
kansa ya sanar da ita damuwarsa, saboda ita ya nuna mata kaguwa da
son sanin damuwarsa zai iya share ta, ta kawo maganar barin
'ya'yansa birnin don zuwa cika aikinsa, ta fahimci damuwarsa ba ta
wannan bangaren bane, saboda haka sai ta tuna da zuwan Abdullahi
bin bin Sharjas da ya zo garin yau kwana uku da suka wuce don haka
sai ta fahimci lallai akwai wani abu dangane da zuwan nasa a cikin
bacin ran Sarki, ta yi nisa ta mika masa wani karamin kofi da yake
cike da tataccen ruwan inibi, bayan ya amsa ta ce "Zuwan Abdullahi
bature
841 Page
bin Sharjas birnin nan ya zo da batutuwa da dama, a game da zargin Waziri Ja'afar, ya sarkin duniya mai kake tunani game da lamarin?" Kamar ta sosa masa inda yake masa kaikayi, ya kurbi lemon ya mika mata kofin ta amsa ta ajiye a gefe sannan ya ce "Rashin
walwalar da nake ciki ta rashin jin dadin jikina a shekaru biyu baya
zuwa yanzu, na kasa katabus a harkokin mulki na ya fara taba min martaba da kima, da yawan mutane suna tunanin na gaza yin riko da
adalci, suna min ganin na gaza samar da ci gaban musulunci, ina damuwa matuka da wanzuwar lamarin da suke zuwa kunnuwana ina
takaici da abu guda, makusanta na basa iya fayyace min duk abin da
yake yawo a birnin bare koma sauran kasashen da muke mulka, har
sakacina ya kai ga mutuwar ga ‘ya'yan Sarki dan uwana suna kokarin kashe junansu a kan mulkin masarautar da muka danka musu
batare da sun zo don a yi musu sulhu ba, mene ne amfanin waziri
Ja'afar da ya zamo wakilina akan komai, mene ne amfani shugaban
dakarun na birni da kauyekan wannan birni har ace kafurai za su kafa
wata rashin gaskiya su aiwatar a cikin kasuwar da afarma mukayi
musu suke zuwa su yi saye hajojinmu, mun yi cece kuce da Hakiman Kauye akan basa bukatar shigowar kafurai amma mun danne su da karfin mulki saboda muna musu fatan samun tagomashi daga ababen
da suke sana'antarwa, kuma ga ni a raye ban mutu ba, mene ne yake
damuna ne? ba cuta nake yi kamar ajali ba, mene ne yake sakani na
zama kamar sakarai".
"Ranka ya dade".
Ta tare shi da murya mai cike da shagwaba, yanga jan hankali
da kuma kwantar da hankalin ma'abocin saurare, ya tsayar da kansa ^
a kanta a nutse yana son ta ce wani abu. "Ranka ya dade" ta kara
maimaita cikin sigar muryar jan hankali “Ka yanke wani hukunci
wadda ya yi min dadin ji a zaman fada na ranakun da suka gabata,
cewar ‘ya'yanka duka za su fara shiga sabgogin mulkinka kai tsaye
bature
85 Page
na tabbata jininka ba zai yaudare ka ko gaza wa da abin da ka umarce
sub a, batu akan Waziri shi ne karfinsa bai zamo kamar na Sarki ba,
amma karfin da ke hannu yaranka tamkar naka karfin don haka ka
yanke hukunci mai kyau, sannan kuma na san tun daga yau in sun iso
za mu samu kyakkyawan labari”.
Ya dan yadda da maganar ta, amma dai ya kalli kansa "Me na
rasa ni da ba zan yi da kaina ba mene ne damuwa ta, lallai zan canza
mai duba lafiyata".
Gabanta ya yanke ya fadi domin hakan na daf da tonowar
asirinta ta ce "Kana zargin wani abu ne?"
"Bana zargin Mustafha da komai face tsufa da kuma kamar
bai da kwarewa a game da abin da ke damuna tunda ba cuta nakeyi ta
rashin lafiya ba, cut ace ta rashin sukuni, karfin gwiwaa, karsashi
shiga kow