NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 29 of 42

Benjamin sai Yarima Yazid ya jinjina kai daga nan kuma sai ya girgiza kai yace "Kayi babban kuskure, ko kana da laifi ko baka da shi, wa'adin mutuwa ya zo gareka, ka jira martani”. Daga fadin haka ya fice daga cikin birnin koda Yazid ya fita sai babban mai kula da cocin birnin dakuma manyan dakaru suka zo gaban Benjamin Babban shugaban coci ya ce "Kayi ganganci ya shugaba, shin baka tunanin matsalar da zata biyo baya". bature 80 Page "Ban so abubuwan nan suka faru ba, domin ba abu ne mai kyau ba, ya ci a ce mun bi shirinmu a hankali, tabbas dole mu kara tsaro da kuma garkame birninmu sannan dole a samu a aikawa da masarauta rum sako". Benjamin ya ce "Masarauta ta gaji da zamowarmu bayin musulunci, ita da kanta ta so mu aikata fitinar da za mu warware yarjejeniya saboda mun tanadi mayaka marasa iyaka za mu iya yaki da su a yanzu". Dukkaninsu suka yi shiru suna nazarin maganganun da yake fada,amma a zuciyarsu suna cike da tsoro domin Sarki Muhammad farsi ba kanwar lasa bane, ba a taba gane shirinsa sai a ranar da ya tunkare ka domin yaki Basu bar wajen ba sai da aka tura sako zuwa rum sannan aka tura sakonne zuwa birane uku da suke makota da su wadanda za su basu taimakon gaggawa kafin isar sakon zuwa rum. ** Al'amarin Jarumi Jarumi Umar lokacin da suka nufo hanyar gida kai tsaye batare da jira ko bata lokaci ba, sai gasu a kauyen Annur cikin annuri akan fuskokinsu, a na cikin zaman yamma na Majalisi sai gasu sun shigo cikin kauyen. Kowa dake cikin kauyen sai ya kasance cikin farin ciki ganin jarumi Jarumi Umar da abokansa sun dawo cikin koshin lafiya batare da an daukowani akan gadon marasa lafiya ba. Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya mike tsaye ya fara furta Shukran ya rabbi, Alhamdullahi, godiya ta tabbata da mai bawa rana Jarumi Umarni ta fitowa da kuma koma, ubangiji mutane da Aljanu mai iko akan kowa da komai, masha Allahu ya rabbi. Lokacin da Jarumi Umar ya karaso ya sauka daga kan dokinsa kai tsaye ya nufi mahaifinsa, ya gaida dattijan fada sannan ya matsa ga mahaifinsa, duk abin da ya faru ya sanar da shi, tun daga bature 81 Page kan tafiyasu zuwa Birnin SHamnun har zuwa lokacin da aka yi kokarin rataye shi, har zuwa da Yarima Abbas ya zo ya kubutar da shi har ma da yadda Abbas din ya gudanar da bincike har ya zartar da hukuncin da yake da ikon yin. Dukkanin jama'ar fadar sun jinjinawa Yarima Abbas kuma sun yi murna da ya zamo aikinsa na farko na matsayin Yarima nuna halin girma da kuma nuna cewarshi jagaba ne mai adalci. Gimbiya Suhaila bin Ababakari na nesa tana hango Jarumi Jarumi Umar jira take yi kawai ya baro fada ya zo wuce wa zai shiga gidata tare shi ta yi masa Magana don jin abin da ke faruwa, aikuwa cikin ikon Allah bisa mamakinta sai ta ga ya yi sallamada manyan fadar Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya nufo hanyar da zata sada shi ga cikin gida. Dukkanin abokansa sun tafi na su sashin da sauri ta nufe shi. Kwatsam ya ganta a gabansa tare da zakuwa a cikin ranta Ya sakar mata murmushi mai taushi, hade da jin kwarin gwiwa samar mata da farin ciki na bata daddan labari. "Dan uwanki yayi nasara zama sarki”. Nan take ta durkusa kasa ta yi sujjadar shukra ta dago tana yiwa Allah kirari da sunayensa tsarkaka kallonta kawai ya tsaya yake yii yana wannan murmushi wadda shi kansa bai san yana yinsu. Sai da ta kamala sannan ta dago ta ce "Da me zan saka maka ya kai Jarumi Umar". Ji ya yi kamar yace wani abu amma sai ya dauke idanuwansa da barin kallonta domin ya fara yi mata wani kallo wadda shi da kansa ya fahimci ya wuce gona da iri ba wacce suka yi sabon da zai mata wannan kallon bace domin a tsakaninsu kawai taimako ne”. "Da ni da ke duk mu godewa Allah mu kuma godewa masarautar Bahara, da yarima Abbas, ban da zuwan da yayi a kan lokaci da tuni na rasa rayuwata". bature Ta kara fadada murmushinta "Kai ne kataimake ni daga fadawa tarkon kafure, ka kubutar da ni daga hannunsu, ka tseratar da rikicin da zai hadu tsakanin kasashen musulunci. Kai ne ka sayar da rank aka tafi kasar da ake neman mai goyan bayanmu, domin su hallaka shi, kai ne ka cancanci yabo da godiya a gare ni, ina mai kara gode maka, kuma watarana zan rama maka wannan halacci" Bai san Gimbiya Suhaila bin Ababakari na da matukar kyau irin na yau ba, sai da ta kasance cikin nishadi tana dariya, koda yake murmushi shi ke tona asirin kyawun dan adam, saboda haka ya zama wani saakarai wajen kallon kyawun fuskarta, har sai da ta tsayar da kallonta a kanshi ta fuskanci yadda yake kallonta, ya dimauce ya kasa samun yadda zai sarrafa kansa har sai da ta dan jima itama tana kallonsa a ranta ta ce Jarumi Jarumi Umar shi ne namijin da take buri ta samu a matsayin mijia gareta yana da zati irin na mazajen gaske dirin jikinsa ya amsa, yanayin jarumtarsa abin burgewa, shine mijin da zai iya kare iyalinsa daga dukkan karfinsa, yana da kirki da kunya kamar yadda take da buri, shi kansa ya manta da yanayin da yake ciki, kwakwalwarsa mai saurin kawomasa shawarwari t
🏠