ladabi
ka kuma lura da kanka da ke kan gangar jikinka, koda na bar
makamina a waje zan iya amfani da naka cikin 'yan dakikai na sare
wuyanka a take a yanzu".
bature
77 Page
Wasu dakaru da suke tsaye a fusace suka motsa suna shirin su
afkawa Zayed, sai Shugaban Benjamin yayi dariya ya ce "Karfin
gwiwarku da kurinku yake tsoratar da matsora ta, na fi ka tsanar
rubutaccen alkawarin zaman lafiya domin bana bukatar zaman lafiya
na fito a kodayaushe na ganni inashawagin cikin musulmi ina cire
kansa kamar ina sassabe a gona, ka yi sa'a saboda wannan
yarjejeniyar zaman lafiyar da baka isa ka fita daga cikin fadar nan a
raye....
Kamar an jefa kibiya daga cikin gwafarta Yazid yayi tsalle
kan Benjamin,dukkaninsu cikin shirin farmakarjuna suke sai shima
Benjamin yayi kururuwa ya taho suka gwabzo, kowa ya ji jikin dan
uwansa,dakarun Benjamin da bawan Yazid kowa yayi yunkurin
tasowa. Benjamin ya daga musu hannu "Kada wadda ya motsa,
wannan bai sabaka'ida ko yarjejeniya ba, yaro ne yake so ya gwada
gwanjinsa don haka ku bar shi”.
Ran Yazid ya kara fusata hankalinsa ya dugunzuma ainun ya
kara farmakar Benjamin akaro na biyu suka kaure da yakar juna
kamar wasu zakaru a fagen fafatawa.
Yazid na da jarumta ta ban mamaki ko da yake dama babu
wani matashi a kasar Bahara da ya kasance rago musamman jinin
sarauta babu takobi a hannunsa, cikin kwarewa ya zare daya daga
jikin wani matashin badakare da ya ZO kusa dank are
shugabansa,amma shi kansa bai san lokacin da
takobinsa ba, saboda tsananin zafin nama.
Yazid ya zare
Suka kaure da yake suna kaiwa juna sara da suka kowa yana
karewa iya karfinsa, idan Benjamin ya matsa kai sara da suka har ya
kusa kure Yazid sai Yazid shima ya kufula ya harzuka ya taso da
nashi sara da suka har sai ya kai Benjamin mukura aka dauki kusan
rabin sa'a batare da wani ya samu lagon dan uwansa ba.
bature
78 Page
Kafin kace mene ne sun zamar da fada tamkar wacca aka
kwana ana yaki, kuma duk da haka ba a samu wani ya samu nasarar
sarar dan uwansa ba, duk irin mugun nufin da suke kai wa junansu.
Tsamari yayi tsamari har ya kai har da yawa daga cikin
manyan dakarun Benjamin sun iso fadar Sarki amma Benjamin ya
dakatar dasu da niyar daukarmataki, a na cikin wannan fafatawar ne
Benjamin ya kuntata Yazid da sara da inda ya kai masa wani sara a
lokacin Yazid ya kwanta a kasa, sun hada kaifin takubbansu inda
Yazid yana kasa yana kokarin yayi amfani da damtsensa wajen
wancakalar da Benjami amma Benjamin ya daddage domin so yake
ya fi karfin Yazid ya ya kais hi karshe ana cikin hakada Benjamin
yaga ya gagara kaiwa ga gaci gashi kuma karfinsa na neman karewa
sai yayi dabara ya zare wata wuka daga kubensaya yanke hannun
daman Yazid. Yazid yayi kara gami da sagewa har Benjamin ya kusa
kai takubban kan wuya Yazid, sai Yazid yayi wata kabbara wani
sabon karfi ya zo masa duk da yankan da yake hannunsa ya fara fitar
da jini amma hakaya wuncakalar da Benjamin ya mike tsaye ya dubi
wajen yankan,amma cikin jarumta ya kara gyara takobinsa ya farwa
Benjamin dake kasa, amma kafin ya kai kansa ya mike tsaye ya zame
banda zamewar da yayi da sara ne mummunan zai tsagashi gida biyu.
Benjamin ya rufo bayan Yazid da niyar ya farmake shi ta
baya, sai Yazid ya wani juye Benjamin ya wuce kamar iska, a
wannan yanayin Yazid yayi amfani da kwarewarsa ya saka takobinsa
ta yanke kuben cikin Benjamin,
Benjamin ya rike wajen ya duba hannunsa yaga jini face face,
yayi murmushi shi ma Yazid yayi murmushi ya ce "Ka ci darajar ^
yarjejeniya da wannan yanka farke cikinka zanyi hatta da hanji su
fito su bata fadarka, to amma ba wannan ne ya kawo ni, na zo gare
ka domin na ji dalilin dayasa kuka farmaki Yar Sarki Ababakari”.
bature
79 Page
Shugaba Bejamin ya jinjina kwazo da bajinta irin ta Yazid
sannan ya ce "Ka koma ka sanarwa da Sarki mun kama ta ne saboda
muna son mu kaita ga Sarki Mu'azzam domin soyayyarta da yake yi
tun shekarun baya da suka wuce, don haka mu a kan kin kanmu ba
mu da wata alaka da ita face hada soyayya tsakaninsu da Sarki
Mu'azzam da ke mulki birnin Sarraf, yarana sun dauketa su kaita
Bahara sannan su dankata da hadiman Sarki Mu'azzamda so kai
masa ita ya aureta".
Koda Yarima Yazid ya ji wannan batu sai ya cika da mamaki
domin Sarki Mu'azzam dan uwan ne ga mahaifina, wadda yake dan
ne shi ga Yayanshi, sannan kuma Sarki Mu'azzam bashi da son rai
yana bin mahaifinsu batare da wata boyayyen munafunci a zuciyarsa
ba, Sarki Mu'azzam ya bada rayuwarsa ga Sarki Muhammad farsi
don haka ya ce "Wannan yana daga cikin aikin shaidanci da fajirci
irin naku, saboda haka karya kake, idan Mua'zam zai nemi auren
'yar Sarki Ababakari, kai tsaye bazai fito ta wannan sigar har ya hada
kai da ku".
Benjamin ya ce "Ji ya zama dole ka bukata na sanar da kai,
wannan matsalolinku ne, kamar yadda aka so ka zo ka ji na sanar da
kai, idan Sarki Muhammad farsi yana bukatar shaidawa muna ita,
domin ba ma yin kwanmu sai da zakara”.
Koda jin wannan batu daga bakin