z aka iya zama Sarkin birni guda ba,
tunda har za ka iya kauda kai a yi duk abin da aka ga dama,saboda
haka baka cancanta da zama Sarki ba kai da duk wadda yake da
hannu a cikin birnin nan za a rufe ku sannan za a rantsar da Yarima
Salman a matsayin sarki a gobe hukunci yana hannunsa"
Koda ya zo nan a batunsa sai ya fice daga cikin fadar
dakarunsa suka bi masa baya. Dakarun da suke bawa Yarima Hilal
tsaro suka dawo bayan Salman.
Bai tsaye ko a’ina sai kofar fada a lokacin da Jarumi Jarumi
Umar ya samu kansa sosai har an bashi abinci da ruwa ya ci ya
koshi, da sauran abokansa, Yarima Abbas ya kasance tare da su, ta
hirar jarumtaka da yadda za a kawo gyara da sauyin tsarin birnin
gaba daya.
Jarumi Umar yayi nisa cike da damuwar abin da yake taba
masa zuciya yace “Ranka ya dade, Kasar mu na cikin mawuyacin
halin kuma tana gab da zubewa matukar aka kasance a haka, ku ne
masu iko da gyara komai na sarauta da kuma juya akalar al'umma
zuwa ga bin tafarkin gaskiya.
A tarihin da muka samu a shekarun baya lokacin da Kakanku
na mulki, babu wani kafiri da ya isa ya shigo cikin birnin Bahara har
bature
72 | Page
sai an yi da shi ya kuma saka hannun cewar ba zai sabaka'idar birnin
ba, ba kuma zai yi shigar banza ba, sannan ba zai yi addininsa a
bainar jama'a ba, a wannan lokaci ba a samun musulmi yana shan
giya, ba a samun musulmi yana canca, ba a samun musulmi yana
aikata zina, musulmai na lokacin Kakanka sun kasance masu
matukar tsoron hukunci, koda a ce babu tsoron Allah a ranka to la
shakka kana tsoron hukunci daga masarauta, masu bin addinin kuma
suna tafiya a tafarki daya babu rabe raben kawuna, idan an ga wata
kowa yana yadda kamar yadda Sarki zai yi bayani, haka zai dauki
azumi kamar kowa, babu malamai masu zuwa da sukar hadisan
manzon Allah sallallahu alaihi wasallam, babu masu zagi da cin
mutumci wasu ahli da manzo ya zauna da su a matsayin 'yan uwa
ana matukar tunkarar birnin Bahara da yaudara domin kowanne
malami ko bayahude da ya yi baddakama ya shigo birnin ya san
karshen kaifin takobi ce karshen numfashinsa, amma yanzu
kauyukan irin namu na tsoron shiga cikin kasuwar birnin domin
tsoron kada yara su dauko munana akidu daga kafirai yahudu, ranka
ya dade yaushe ne wannan makircin da yahudu ya shiryawa birninmu
zai kau daga doron kasa.
Maganganun sun shiga zuciyar Yarima Abbas kuma ya ji su
har cikin ransa, tabbas Jarumi Umar bashi da tsoro ko fargaba kamar
mahaifinsa, domin dukkan mutanen birnin suna tsoron zuwa yiwa
Sarki wannan tambaya amma sun kasa, sai Abdullahi bin Sharjas ne
kadai yake iya gaba da gaba da Sarki ya gaya masa gaskiya, yau
gashi dansa bai ji shakkarsa ba,shi maya tare shi ya sanar da shi.
"Lallai komai yana da lokaci, kuma yana da karshe, insha
Allahu za mu yi maganin komai da yaddar Allah. Yanzu na san a
kagauce kuke da kuka ma hanya don komawa gida. Za ku iya tafiya,
Ya kai Jarumi Umar ina son sanar da kai cewar a duk lokacin da na
bukaceka da kai da abokan tafiyarka lallai na ji dadin kasancewa tare
bature
2
73 | Page
da ku,domin a rayuwata na tsani munafunci, kuma ina son mutum
gaya min gaskiya duk dacinta, saboda hakaina bukatarku a tare da ni,
kuma ina nan zan kawo maku ziyara bayan na kamala da ayyukan da
mahaifina ya sakani".
Suka jinjina kai alamar gamsuwa da maganarsa. Jarumi Umar
ya ce "Na ji dadin yadda ka gyara lamuran birnin SHamnun a
kankanin lokaci, ina fatan ka taimakawa Sarki Muhammad farsi a
dukkan tafiyar da lamuran kasarsa Allah ya taimake ka"
Yana fadin haka suka mike tsaye Yarima ya dube su "Insha
Allahu za mu yaki kafirai kafada da kafada tare da ku, za mu
fatattake su daga birninmu insha Allahu, Allah ubangiji ya tsare
hanya".
Suka amsa da amin su dukansu sannan suka nufi hanyar fita
yana tsaye yana kallonsu, yana ji a ransa akwai nasara a rayuwarsa ta
zama Sarki a haduwa da ahlin Abdullahi bin Sharjas, domin ya
fuskanci ta inda zai gyara tafiyar birninsa ta hanyar shawarwari ga
mahaifinsa sannan kuma ya samu tsakwakuren da zai yi tare da su
har suka fice yana murmushi.
**
Wata irin bakar runduna ce mai tsananin yawa ta taso daga
yammacin birnin Bahara, wasu gungun bataliyar dakaru ne iya
ganinka rukuni rukuni sun kai rukuni goma, duk rukuni daya z aka
tadda su birjik kamar gudaje, sanye suke da bakaken kaya da aka
sana'antashi da batar bakar damisa, idanuwansu jajaye da hula na
akansu wadanda suke da kahon saniya guda daya daya a tsakiyar
goshinsu.
Dawakansu ma bakake ne wuluk babban cikinsu na tafe, yayi
wasu zaneka da baki a kan fuskarsa wadda alamun hakan yaki ne
labbansa bakinkirin, yana muzurai yana zare ido.
bature
74 Page
Babban Dakare na kare dange daga cikin Dakarun Hangalawa ne ke tafe a gaba da kamar taku shida sannan dakarun nasa na biye da shi a baya kato ne na gaske, haka dokinsa jibgege ba karamin namijin gaske bane zai yi idi biyu da wannan katon bai koma da bay aba, yan da suma kamar mahaukaci a kansa sannan akwai wata
jelargashi guda daya ta ka har gadon