NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 25 of 42

a yasa na samu kurewar lokaci ban shigo birnin nan ba a daren jiya, sannan na samu aiko da sako zuwa ga wasu yan majalisar Sarki don su shaidamin dalilin da yasa yarima Salman ya gudu, na samu dukkanin labari, abin da ya faru, sannan dukkanin alʼamarin da ya faru na samu hujja mai karfi wacce zan iya yanke hukunci kai tsaye, amma bisa adalci ba zan yanke hukunci kai tsaye akan ku ba, saboda laifinku na tilastawa ne ba kamar Waziri ba da na samu dumu-dumu da laifi barkatai, "Ka shigo min yarima Salman". Ya dubi daya daga cikin dakaren da yake tsaron lafiyarsa. Kai tsaye dakaren ya tafi zuwa bakin kofar fadar yana zuwa yayi Jarumi Umarni da hannu aka shigo Yarima Salman cikin fadar. A nutse yake bature 68 Page 69 Page tafiya cikin izza ta mulki babu tashin hankali ko firgici a tare da shi, ya zo gaban Yarima Abbas ya tsaya cikin girmamawa, Yarima Abbas ya dube shi cikin kulawa sannan yace "Me yasa ka bar birnin Shamnun "Na bar birnin Shamnun wane dare da na kwana da zargin cewar akwai makarkashiyar daga fada, na gano cewar an shirya hallaka ni ne, saboda yadda na isa sansanin dakaru, na duba yadda su ka amshi ne a matsayina na wadda mahaifina ya bar suna na a matsayin magajinsa, har sai idan akwai wani abin cutarwa da na taba aikatawa bayan ba ransa kafin nadin sarauta, na shirya zama da yan Majalisar dattawa na gidan Sarauta, ban samu hadin kan kowa daga cikinsu ba, sai wasika a cikin dare da wani daga cikin majalisar dattijai ya turo min da ita" Koda ya zo nan a zancensa sai ya dauko wannan takardar da aka rubuta wasika ya fara karantawa don kowa ya ji Ka bar birnin Shamnun a daren yau, ka da ka bari ka kwana, babu yadda za mu iya ta dole da sa hannun kowane dattijon majalisa saka hannu a kashe ka bisa zargin da za a dora maka na cin amanar kasar wadda za a turawa Sarki Muhammad farsi a matsayin laifi. Bai bayyana ko wane ne shi ba saboda tsoro na so nayi tirjiya na dake na ki guduwa amma kuma sai na tuna matukar bakuna sun hadu to bani da wani karfi da zan iya tunkarar su, sai nayi amfani da wannan shawara ta wannan mai turo min da sakon takarda na bar birnin, haka kuma ya kara tura min sakon na janye yar uwata daga birnin Shamnun saboda ana kokari ayi amfani da ita don gano inda kake, wannan dalili yasa na bar birnin nan nab ace cikin wani rukunin kauye a cikin birnin Shamnun yadda babu wadda ya isa ya gano inda nake, sai a lokacin da nag a tawagar Yarima Abbas na daren jiya na bayyana a gare shi domin zayyane masa dukkan abin da ke faruwa. bature 70 Page Koda Yarima Salman ya gama jawabinsa, sai yarima Abbas ya juya kan yarima Abu Kausar yace "Kana da damar da za ka fadi albarkacin bakinka". Shugaban zauren majalisar dattaje abu Kausar ya mike tsaye gami da cewa "Mun yi babban kuskure a bisa al'ada na dan adamda tsoro yake bin jinin jikinsa da son duniya, na yabawa dattijai na karkashina da a karon farko sun turje, duk da cewar an dauki silalla masu daraja an basu, an kuma yi musu alkawarun masu nauyi duk da hakasun turje sai akafarayi musu barazanar kisa, sannan aka hana tura mu sako ko kuma fita daga birnin ta kowacce hanya, ni ne nayi amfani da wani bawa na da babu wadda ya san shi nake aikawa Yarima Salman sako, sako na farko da na biyu, mun gaza a matsayinmu na masu karfi a masarauta, mun saka tsoro a rayuwakanmu, na so mun jajurce koda za a jininmu zai zuba a doron kasa amma dayake mun yadda Allah daya ne kuma zai kawo mafita sai muka dage da addu'a Allah ya wargaza wannan al'amari, a kullum mukan hadu mu sauke alkur'ani mai girma, babu taba gajiyawa ba, cikin sauki Allah ya kawo mana mafita, ya kai Yarima mai daraja, muna sanar da kai babu wani ko wani da ya ci koda daya daga cikin sulallan da suka ba mu, sannan muna farin ciki a yi gaggawar yi mana hukunci mafi dacewa saboda mu masu laifi ne". Koda ya zo nan a zancensa sai Yarima Abbas ya jinjina kai gami da duba lamarinsu da kuma kokarinsu na kai kuka ga ubangiji, sai ya ce "Na bar lamarinku ga mahaifina, domin bazan iya yanke wannanhukuncin ba, a kai tsaye zan iya yi muku adalci, amma ban sani ba ko masarauta za ta iya yafe wannan laifin amma a bangarena na jinjina muku”. Sai a wannan lokacin Yarima ya koma ga Yarima Hilal ya ce "Me z ace dangane da al'amarin da ya afku, shin akwai sharri ko kage a ciki?" bature 71 Page Yarima Hilal yayi shiru kansa a kasa daga bisani ya dago kai ya dubi Yarima Abbas yace "Ba ni da wani kudiri da na kunsa a raina illa na gaji mahaifina, dalilina kuwa shi ne tsoron makoma ta da kullum ake tsorata ni da shi shi ne idan Yarima salman ya zama Sarki zai kashe mahaifiyata, sannan zai kashe ni da yan uwana, saboda tsoron za mu zama barazana a gare shi, na yadda na amince cewar zan zama Sarki amma ba hannu na a cikin duk wadannan al'amarin da aka aikata na bada sulalla, na yunkurin kashe yarima Salman, da ma tara dattijai domin tilasta su, abin da na yadda da shi zan zama Sarki wannan kuma shi ne fatana". "Tun anan ta tabbata ba
🏠