NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 24 of 42

shiga bangaren sarautar gidan. Bai tsaye ko ina ba sai karagar mulkin gasar Shamnun. Babbar fada da ce da aka kawatata da gini na alfarma waje ne mai girman gaske, da yake mallaki ne na Rum, a shekaru masu yawa kafin yaki sarkin wancan zamani a dawo da ita karkashin ikon musulmi sun yi matuka batar da dukiya da basira wajen gina wannan fadar can nesa kujerar mulki take, sannan daga hagu da dama akwai kujerun alfarma na waziri dakuma Babban Dakaren birnin sannan ga bature 66 Page 'yan majalisar sarki su ma kujerunsu da aka kerata da zallan zinare a shimfide sahu sahu a gaban kujerar Sarki. Kai tsaye Yarima ya je bakin kujerar mulki ya zagaye ta wajen sau uku kafin ya samu wajen zama. Ya zauna sosai yana kallon kofar shigowa wacce take kallon saitin kujera bai dauke idanuwansa daga wajen ba har sai da Yarima Hilal da kuma Waziri suka shigo cikin fadar. Ganinsa a kan karagar mulki duk hankulansu ya ta shi ainun suka tsorata matuka. Ba wani abin tsoro bane domin wani mai babban matsayi ya zo karamar masarauta ya zauna a kujerar mulki hakan dama yana faruwa, idan Sarki Muhammad farsi zai je kowacce kasa da take karkashinsa shi ne zai gudanar da komai har ya bar kasar, amma abin da yasa suka tsora a wannan lokaci suna jin cewar Sarki Muhammad farsi ya aiko dansa Yarima Abbas ne domin ya kwace masarauta a datseta, har sai an kamala bincike wadda hakan idan ya faru, babu shakka sai sun rasa kujerar mulkinsu, domin za a iya dauko wasu daga cikin jinin sarautar a basu tun da sun kasa daidaita kansu. Waziri Adnan ya kara so cikin sunkuyar da kai kasa shima Yarima Hilal. 'Ranka dade ina mai maka maraba da zuwa birnin Shamnun". Yarima ya kalle shi cikin nutsuwa. Ya mayar da kansa kan Yarima Hilal Yarimaya dube shi a dari dari “Barka da zuwa dan uwana Yarima Abbas". Yarima Abba yace "Na zo takasanas daga Babban birnin zuwa birnin Shamnur domin aiki mafi muhimmanci a gare ni, na zo domin na fitar da gaskiya na kori karya, kuma nayi alkawari ba zan bar birnin ban sai na tabbatar da adalci, na kuma danka mulki ga wadda ya cancanta. Yanzu mene ne laifin Jarumi Umar da kuka yi kokari kashe shi? Shin baku san waye shi bane?" bature 67 Page Waziri ya dago da kai a tsorace ya ce "Ranka ya dade ba mu san wane ne shi ba". "Shin bai sanar da ku ba?" Waziri yayi shiru har sai da Yarima Abbas ya kara maimaita tambayar, sannan ne Waziri Adnan ya ce "Ya sanar damu amma saboda halin da muke ciki na bukatar Yarima Salman da tsoron shirin da zai zo mana da shi ya sa muka yi tunanin karya ya shiryo mana don ya samu ya kawo mana sharri cikin masarauta”. Yarima Abbas ya jinjina kai “Wane bincike kukayi domin ku tabbatar da hakikanin gaskiyarsa ko akasin haka?" Waziri Adnan yayi shiru domin bai da tacewa "Mun yi babban kuskure ranka ya dade a gafarce mu?" Yarima Abbas ya mike daga kan kujerar mulki Shamnun ya nufo inda waziri Adnan yake yana cewa “Kai ne magajin birnin Shamnun, kai ne abokin Sarki Kawu na Ababakari shekarunka sun yi tasirin da zaka wanzar da masalaha a tsakanin wasiyar da Sarki ya bari, kai ne za ka yi bi duk hanyoyin da za yiwa 'yan uwa juna adalci, amma kai ne mai kuskure aiwatarwa, da ace a lokacin yarima Hilal ya fara mulki ne za a iya yi masa afuwa bisa ajizanci da kuma girma irin na sarauta da rashin kwarewa zai iya kuskure, amma babu wani abu da baka sani ba, saboda haka baka cancanta da zama Waziri birnin Shamnun ba”. Ya zube kasa ya fara neman kama kafafuwan Yarima Abbas "Kayi hakuri ranka ya dade shekaru ashirin ina kan matsayina ka tausaya min na mutu, ina zan kai darajata kima da ake kallo na da shi a cikin birnin na". “Ka koma ka yi bautar Allah kajira lokacin da Allah zai dauki rayuwarka, ko ka samu ka rabauta zuwa ceton Manzon Allah amma babu wani dalili da me kuskure irin wannan ya ci gaba da zama waziri birnin Shamnun." bature Dakarun hudu suka shigo cikin fadar suka bambare shi daga jikin yarima Abbas suka fitar da shi yana ci gaba da magiya amma Yarima Abbas ko kallon inda yake bai kara yi ba. Ana fita da shi sai ga dattijan birnin sun shigo wadanda suke da alhaki akan zaban Sarki, Yarima Hilal yana dubansa gabansa, sai da suka gama shigowa suka samu waje suka zauna sai Yarima Abbas ya fara tafiya cikin takama da izza irin ta saraki, har sai da ya ya isa inda suke kansu a sunkuye alamar girmama Yarima Abbas. "Ina Adalcin ku, ina iliminku, ina tsoron Allah da shi ne ya baku cancanta aka dauki kujerun nan aka baku, tabbas kun ci amanar Allah kuma kunci amanar masarauta dole sai hukunci ya tabbata a gare ku, domin ba ku zamo adalai kamar yadda ake tsammani ba." Shugaban Dattijan majalisar Abu Kaisar yayi ajiyar zuciya gami da "In an bani izini ina da Magana." Yarima Abba ya dube shi ya ce "Da sauran lokaci kafin wani ya yi Magana". Abu Kaisar ya jinjina kai gami amsawa da girmamawa. Yarima Abbas ya dubi yarima Hilal yace da shi "Na yi kokari gano inda Yarima Salman yake boye a jiya da yamma shi ne dalilin d
🏠