uro mata wuta
cikin tashin hankali ta yi watsi da wani karamin ma'adanin
abubuwanta komai dake kan abin ya waste ta kara rusa kuka mai
tsanani ta fada kan shimfidarta.
Babu wacce ta isa ta auri Jarumi Umar matukar tana raye, sai
ta yi sanadiyar kashe ta, it ace zata auri Jarumi Umar duk rintse idan
kuwa bata aure shi ba to kuwa sai dai su rayu a haka, babu wadda zai
yi aure.
A bangaren dakin da Suhaila bin Ababakari suke Uwar gida
Kubra na tsaye a kanta don kwantar mata da hankali "Kiyi hakuri ki
bature
62 Page
kwantar da hankalinki babu wani abu haka take bata da nutsuwa
akan komai kuma zan tsawatar mata".
Suhaila bin Ababakari ta dubi uwargida Kubra ta kuma
fahimci abin da take kokarin yi na son kwantar mata da hankali ta ce
"Ba wani abu Mama, ko ubangijinmu baya kama dan adam da laifin
cikin rashin sani, wannan ba komai bane, akwai damuwa sosai rasa
jarumi kamar Jarumi Umar a cikin al'umma, na fahimci damuwarta
sosai kuma na yafe mata".
Uwar gida Kubra ta ce "Kina da zuciya mai kyau, nagode da
fahimta, in kin kimtsa idan Hakimi ya fito fadar tsakar gida ki je ki
gaida shi".
Gimbiya Suhaila bin Ababakari ta jinjina kai alamar zata je.
Sannan ne uwa Kubra ta fita daga cikin dakin ta kuma nufi dakin
Hamdiya tana kwance tana garzar kuka ta zauna kusa da ita.
"Ban san me yake damun zuciyarki kike bijirewa koyarwar
mu ba, akodayaushe muna koyar da ku muhimmancin bako a
wannan masarauta amma bakya ji, duk ranar da za a yi bakuwa
komai girmanta ko matsayinta sai kin nuna mata halinki na rashin
kauna, ki saita zuciyarki ki iya mu'amalar kirki da mutane
musamman 'yan uwanki mata ace a duk fadin garin nan da wajensa
baki da wata kawa ko aminiya, ke kullum cikin rigima kike da 'yan
mata, dan Allah ki gyara halayenki ki guje abin da zai sa na kara
dora hannu akan fuskarki, kin san ina son ki, ina kaunar ki ko da ba
ni ce na tsuggunna na haife ki ba, ina jin matsananciyar damuwar da
kike ciki".
Idan kina jin damuwar da nake ji da tuni kin tilasta aurena da
Jarumi Umar tunda kin sani sarai babu wani mahaluki da nake so in
ba shi ba
Ta fada a cikin zuciyarta har Kubra ta gama yi mata nasihar
ta gaji ta fita ba tace mata ta tafasa ba, jira take ta fita ta bata guri
bature
631
64 | Page
domin ta fara shirin da zata yi domin kawar da Gimbiya Suhaila bin
Ababakari.
Aka dauki Jarumi Jarumi Umar zuwa cikin dakin magani
cikin sauri da gudu gudu, da fari aka fara da zuba masa ruwa domin
ya dawo hayyacinsa, cikin ikon Allah numfashinsa ya dawo a
hankali, suka dinga godewa Allah, a hankali ya fara budewa
idanuwansa ya ganshi tare da abokansa duk fuskarsu hawaye ne ke
kwaranya. Batare da sun lura da ya bude idanuwansa ba, daga can
suka ji muryarsa na amsa amo da cewar "Na gaya muku zuwan
mutuwa a gare ni ba sauki bace".
Suka dube shi cikin farin ciki da annushuwa murmushi yake
yana shafa wuyansa saboda zafin da wajen yake masa ga shati sosai
wajen yayi jawur.
"Su ka hada baki saboda duk wasu lokutan da ya kutsa hadari
ya samu ya kubuta irin Kalmar da ya kesanar da su kenan cewar
Zuwan mutuwa ba sauke ce a gare nib a, maʼana mutuwa ba za ta zo
ta dauke shi cikin sauki ba, sai an sha artabu, wannan addu'arsa ce ta
neman yaddar Allah akan yay i mutuwa a cikin abokan gaba yana
yaki domin daga Kalmar Allah".
Suka rungume shi, har sai da mai saka masa magani ya gama
hada maganin sannan suka rabu da jikinsa ya saka masa maganin a
wuyansa.
F
"Me ya faru?"
Ya yi musu tambayar a lokacin da ake saka masa magani.
Adai-dai wannan lokacin Yarima Abbas ya shigo cikin daki da
dakaru na biye da shi. Ya kara so duk suka zuba masa idanu, har ya
kara so kusa da Jarumi Umar ya zauna ya mika masa hannu domin su
bature
65 Page
yi musabaha Jarumi Umar ya dube shi da mamaki ya ce "Ranka ya
dade"
Bai dauki hannun ba ya kara jinjina kai ga Jarumi Umar
domin ya aminta su gaisa. Jarumi Umar ya mika masa hannu cikin
girmamawa shi ma yarima ya amsa yana mai cewa "Mahaifinka ya
sanar da ni cewar nayi kokari na kubutar da kai daga sarkakiyar dake
cikin kasar nan. Lallai Allah ya nufa da kwanan ka a gaba”.
Jarumi Umar ya dube abokansa alamun tambaya domin bai
san cewar yarima ne ya cece shi ba, suka daga masa kai alamar
tabbatarwa. Jarumi Jarumi Umar ya jinjina kai “Ina godiya ranka ya
dade, ya mahaifina yake dafatan yana cikin koshin lafiya?"
"Yanzu haka ya koma gida tun jiya mun rabu da shi, kuma ya
san da cewar kana cikin hadari tun da ya fuskanci Waziri Ja'afar ya
san cewar ka taho birnin don haka da zan zo nan ya bani amanarka,
nagode wa Allah da ya sa na riske ka a kan lokaci.
Yanzu abin da nake da bukata da kai ka kwanta ka samu
hutawa, duk wani abu da za a zartar da shi ko fahimta a birnnin
Shamnun yana gare ni, kuma zan aiwatar da shi bisa yaddar Allah,
wannan nauyin mahaifina ya dora min kuma shi ne gwaji na farko
daga samun nagartar sarauta ta”.
Yarima Abbas ya mike tsaye cikin sauri ya juya ya fita tare
da dakarunsa ya barsu a tsaye anan. Kai tsaye ya