NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 21 of 42

cikin tsana abokan tafiyarsa a dai-dai lokacin Mu'az ya kasa jure wa yayi kukan kura ya kwalla kabbar, dukkanin su uku suka zare takubbansu suka dauki kan Jarumi Umar. Dakaru suka sha kanšu suka tare su ana kokari fara dauki ba dadi. Wata kibibiya kamar walkiya ta ta wuce ta saman kawunan mutane daidai igiyar da aka daure Jarumi Umar ta shigar burgu ta yanke ta, kai kace takobi aka saka aka yanke igiyar, Jarumi Umar ya fadi kasa ko shurawa baya yi. bature 56 Page 57 Page Sarauniya Ruma da Waziri suka mike da kallo cikin kaduwa da tunanin waye ya zo ya katse wannan al'amari. Idanuwansu akan Yarima Abbas yana tsaye da kwari a hannunsa idanuwansa na kallon gangar jikin Jarumi Umar. Koda ganin Yarima Abbas sai kowa dake wajen ya rissina kai kasa alamar girmamawa, hatta Waziri da Sarauniya Ruma, sai da suka sunkuyar da kai kasa, cikinsu ya duri ruwa. A Wannan lokacin Mu'az da su Dawan suka yi sauri suka ratsa mutane suka isa kan gawar Jarumi Umar suna masu ihu da kururuwa. Dawan ya fada kansa ya dago shi ya cire masa bakar hular rufe fuska da take sanye akanshi, duk ya hada majina idanuwansa sun yi tulu-tulu kamar zai zazzago. Dawan ya saka hannunsa kan jijiyar wuyansa. Saklahu ya saka a hannunsa, duk su biyu suka fara wata irin fara'a kamar wasu ciwon hauka, "Yana raye yana raye yana raye, haka suka dinga maimaita. Muaz ma hannunsa ya saka ya ji, yana tabbatarwa ya saba shi, a kawo agaji yana daye yana raye. Waziri ya karaso ga Yarima. Yarima bai dube shi ba, idanuwansa na kan Jarumi Umar da ake kokarin ceton rayuwarsa. "Yarima...." دو Yarima ya katse shi da cewa “Ka je ka yi kokarin ceton rayuwar Jarumi Umar kafin ka zo mu yi Magana duk wani likitan da ka san kwararre ne ka neme shi domin ku ceci rayuwarsa. ** "Ki ta shi❞ Wata murya ta tashe ta, a cikin baccin da take cikin dare, ko da ta mike zaune sai ta ga dakin babu kowa,tabbas kuma ta ji an tashe wani haske ta hango daga bakin kofa tana tsayar da hankalina wajen ta hango wata kyakkyawarmace sanye da fararin kaya sannan bature • 58 | Page haske har daukar ido yake, ta mike tsaye budurwa ta ce "Ki zo in sada ki da dan uwanki Salman". Ta fada da daddar muryarta, kafin ta yi mata tambayar budurwa ta yi gaba ita kuma sai ta ji tana mai bin bayanta har suka fita daga cikin daki ta fito waje babu kowa a farfajiyar gidan Hakimi Abdullahi bin Sharjas, abin da ya bata mamaki ke nan. Babu masu tsaron dare bare na safe babu kowa sai kukan tsuntsaye ta so ta gaza bin bayan budurwa amma tazarada ta bata ya sa takeson ta ji me ke tafe da ita. Don haka ta kara sauri dan ta cimma ta. Koda ta ci gaba da binta a baya har suka yi nisa can nesa kadan sai wannan budurwa ta kyakyace da dariyar mugunta. Jin wannan dariya ya sa Gimbiya Suhaila bin Ababakari ta dago da kanta cikin mamaki sai ta ga wajen ya cika da mutane sannan ga wani mutum a gaban rundunar dakaru sama da dubu sun sashi a gaba daure yake da sassarin bakin karfe hannu da kafa, fuskarsa a rufe ba a gane ko waye shi. Tana tsaye ta zuba ido gabanta yana faduwa sai wani mahayin doki mai suffar kafurci ya bayyana a bisa dokinsa yana zagaye wannan mutum da yake a daure, har sai da ya zagaya shi sau uku ana hudu ne ya tsaya ya saka kaifin takobin nasa ya cire wannan hular da ta rufe wa mutumin fuska sai ga Jarumi Jarumi Umar ya bayyana suka yi kallo kallo da shi idanuwansa na zubda hawaye. Ta tawo da gudun don ta zo inda yake amma kafin ta zo wannan Katon Sadauki ya saka takobinsa ya cirewa Jarumi Umar kai, jinin yayi tsartuwa har ya bata mata fuska. Ta kwala wała mahaukaciyar kara mai amsa kuwa da amon. Tana ji tana kallo gangar jikinsa ta sulale kasa, haka kansa yayi katantanwa a gabanta, da ta durkushe a kasa. Kafafuwanta sun kasa daukarta. bature 59 Page "Jarumi Umar Jarumi Umar! Jarumi Umar!! Ta kwala kiran sunansa sau uku. Firgigit ta farka daga bacci mai nauyi ne ya dauke Gimbiya Suhaila bin Ababakari bayan da ta idar da sallar asuba, ta yi sa'ar gaske da ta samu wannan bacci tsawon lokaci da ta dauka bata samu kanta a wannan halin ba, don haka babu ma wadda ya tashe ta ko don ta je ta gana da Abdullahi bin Sharjas domin jiya ya dawo a ciki dare. Ta farka a razane a tunaninta abin da ya faru yana nan a zahiri don hakada gudu ta fita, Kuyangarta Rumaisa, ta riko hannunta, ammaina ta kwace tana za su kashe shi. Tana fita sararin tsakar gidan taga ana ta aiki irin wanda aka saba yau da gobe batare da wani tashin hankali ba. Addu'a ta fara yi tana sauke numfashi kasa kasa. Kubrat dake bada Jarumi Umarni ta lura da ita. Gimbiya Suhaila bin Ababakari tana ci gaba da addu'a har ta samu nutsuwa acikin ranta ta tabbatar da ba gaskiya bane abin da ya faru da ita mafarki take yi. Akwai wata budurwa da bata wuce sa'ar Suhaila bin Ababakari ba, ana mata lakabi da Hamdiya, Hamdiya wato kyakkyawar budurwa ce da ta zama ‘yar riko a hannun Kubra, tun tana da kuruciyarta, yar aminin Abdullahi bin Sharjas ce da ya rasu tun tan
🏠