in musulunci saboda cudanya da kafirai
yasa al'adunsu suka fara sauya wa hatta masarautar ta rage tsananta
wasu abubuwa da suka zama haramun.
Abubuwan na faruwa da yawan yan Kasar suna kokawa
musamman yan kauyukan da abin bai shafe su sosai ba, sai dai ta kai suna iya hana matan su da samarin su zuwa birnin Bahara saboda
tsoron juyewar tunani to amma hakan ba kara min tauye su yayi
saboda ya rage musu kasha hamsin cikin dari na tafiyar da
kasuwancinsu saboda samari su ne masu karfi a jika wajen tabbatar
da nasarar su a kasuwanci.
Sun Kai korafi ga Sarki Muhammad farsi salahudden amma
saboda kutse da nasara wa suka yi wa maasarautar ya kasa aiwatar da
komai duk da cewar Sarki ne adali mai kokarin ganin ya tafiyar da
adalci a mulkinsa
Babban sakacinsa amanna da wasu jigajigan fadar sa
wadanda sune suke tafiyar da komai na mulki, sai abin da suka so ya
ji,
Karku manta mun kira wata kabila a baya wacce ita ce kabila
mafi yawan mutane a cikin birnin Bahara amma kuma ita ce kabila
mafi riko da addinin musulunci saboda an samu manyan malamai da
suka taso a cikin kabilar marasa adadi wannan kabila ana kiran ta da
Kabilar Nur, dan haka ana kiran kauyen Annur. Kauye ne mai
dimbin tarihi wadda ya bar baya mai cike da alfahari, basu kai sauran
kauyuka birnin Bahara yawan mutane ba amma sun fi kowane Kauye
karin suna hatta a fadar sarki baka jin kalmar kowane Kauye face
Annur haka zalika munafukai masu yin zagon kasa suna ambaton
bature
4|Page
kauyen Annur a kowane lokaci, takororinsu kauyuka masu yin
hassada da kauyen suma suna ambaton kauyen Annur.
Abdullahi bin Sharjas Ibn Abdullahi kuwaif shi ne Hakimi
kuma jigo a cikin Hakiman Kasar Bahara.
Yana da shekara saba'in da bakwai. Yana da yaya takwas sai
da ya haifi yaya har biyar mata sannan ya haifi maza uku. Kubra ita
ce matarsa ta farko wacce suka yi gwagwarmaya rayuwa da ita, ita ce
take da mata hudu maza biyu, sai uwar gidan da take da mace daya
namiji daya, Ana mata lakabi da Humaira ibn Sa'ad
Yayansa maza biyu gwarazan jarumai ne masu kaunar ci
gaban musulunci, Babban shi ne Ahmad Abdullahi bin Sharjas
Abdullahi Ibn Kuwaif sai Jarumi Umar Abdullahi bin Sharjas
Abdullahi Ibn Kuwaif matasa ne masu karfi a jika, masu iya sarrafa
duk wani nau'in makami, masu hikima da basira.
Ahmad yana tsaka da horor da mata sa salon yaki a daidai
lokacin da yake cewa "Duk lokacin da yaki yayi tsamari ya zamana
kun, zamo yan kalilan a gaban abokan gaba kamar sun ninka ku sau
uku a hankalce ba za ku tsaya ku ci gaba da fafatawa da su ba, domin
za su yi galaba akan ku, abu na farko ku yi wa jagoranku inkiya don
ya hankalta domin yayi muku izinin ja da baya"
Da gudu wani mahayi ya shigo cikin filin a bisa ingarman
Dokinsa, yana zuwa batare da dokin ya tsaya ba ya dira gaban
Ahmad ya sallama gami da gaisuwa irin ta jarumai ya ce "Yarima
sako daga Yarima Jarumi Umar cewa ya bi sahun wasu daukacin
kekunan doki da suka fito daga Garin DURSA sun nufi babban birni,
ya shaida min cewa lallai yana bukatar mayaka su biyo bayansa.
Koda Ahmad ya gama jin haka sai ransa ya baci ya ce cikin bacin ra
"yaushe ne Jarumi Umar zai daina dauko magana, menene abin da
yayi masa zafi da kafiran Dursa da babbar birni".
Kowa yayi shiru yana sauraren Jarumi Umarni Ahmad kadan
ya ce "DAWAN yanzu shi da su waye tare na ga abokan tafiyar sa
suna muhallin su".
DAWAN ya gyara tsaiwa ya ce, daga ni sai shi muka fice tun
safe ayarin ne suna da yawa akalla mahaya doki ashirin na kasa
bature
5 Page
goma, tare da makamai don haka ya ce lallai sai dai ni na zo don shi
ba zai iya bari su bace masa ba don basu tare da`alkairi".
Ahmad ya ce "Maza ka sanar wa da abokan sa, ku yi gaba ni kuma
zan sanar da Sarki".
Kai tsaye Dawan yayi sauri ya tafi wajen abokansa dan sanar
da su hali da Umar yake ciki.
***
Wani kyakkyawan saurayi ne, mai tarin kyawu da zati irin na
mazaje yana da tsananin kwarjini shekarunsa za su tasarwa ashirin da hudu, Dokinsa wani ingarma ne ya zauna cif cif da shi kayan sulki ne
a jikinsa da takobi rataye a kugunsa, sai kibiya a kafadarsa ya rataya
ta. Ta cikin ciyayi yake bin sahun kafiran Darsun sannu a hankali
yadda ba za su gane ana bin sahunsu ba, daga nesa yana hango yadda
lamarin ke tafiya.
**
Duniya dole ne ta zama tamu, idan har muka bar yakar
musulunci muka juya baya tabbas za su ci gaba da yaduwa a doron
kasa su ci gaba da mamaya, saboda haka dole ne mu kashe
sarakunansu, manyan malumansu mu dasa mugun rikicin a cikin
yankunnansu, mu kwashe dukiyoyinsu, mu zamar da su bayinmu
abin bautarwarmu a doron duniya, Wannanshi ne yakin da zamu yi"
Koda Sarkin JARMUR JAKUB ya tsaya a nan a bayaninsa da
yake guduna a karkashin sarakunan Kiristoci sai ya dube su daya
bayan daya yana mai nuna su da hannunsa cikin izza da isa gami da
kasaita.
An halicci duniya domin mu ne, ba domin su ba, domin mu
ke da mafiya yawan Annabawa muke da yawan lardinai mafi kyau,
muke da fikira, mu ke da gine-gine mafi kyau, su bayi ne namu,