NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 17 of 42

rsa, yanzu ba mu da abin da zamu iya sai mu jira zuwa anjima mu ga ni". Lokacin da Dakaren ya shiga wajen Waziri Adnan a lokacin yana tare da wasu dattijan kasa ana shirin yadda za a cimma nasara wajen dora Yarima Hilal a kan karagar mulki a gobe, sai ga sakon zuwan dakaren kofa,, ko da jin haka sai ya dakatar da bayanin da yake domin ya san akwai babban al'amari. Koda ya fito sai shugaban dakaru ya zayyane masa duk abin da ya faru har ya shaidamasa yanzu haka yana hannu mun tsare shi". Koda waziri ya ji wannan batu cikin gaggawa yayi gaba don zuwa kurkuku domin ya je ido ya gane ya kuma tabbatar da zargin da ake yi. Koda suka isa kurkuku sai masu tsare wajen suka fito da Jarumi Umar suka gurfanar da shi gaban waziri suna mai dukar masa da kai kasa. Waziri yayi dariyar keta yace "Ku kyale shi, ai bako ne kuma ba mu da tabbacin abin da ke tafe da shi." Suka sake shi Jarumi Umar ya dago kai ya dubi Waziri Adnan ya ce "Ka sada ni ga Sarki Hilal domin ina da sakon gaggawa a gare shi, kafin wata matsala ta biyo baya". Koda Waziri ya ji wannan batu sai ya gigiza kai yana dariya ya ce "Me ke tafe da kai ga Sarki?" bature ? 46 Page Jarumi Umar ya girgiza kai ya ce "Da ace sakon naka ne da zan sanar da kai amma tun da har wannan sako ba naka bane, babu dalilin da zai san a sanar da kai". Waziri ya ce "Ashe ba zaka rayu ba, matukar baka sanar da ni , to ka yi sani cewar rayuwarka tana kan gargara”. sakon Sarkiba Jarumi Umar yayi murmushi ya ce "Kamar yadda taka rayuwar take kan gargara, bari in baka wani labara kadan mu biyar ne ke dauke da sako zuwa ga Sarki, ragowar hudun suna kokarin ganawa da Sarki akowane lokaci idan sun hadu da Sarki za su bashi labarin cewar kana tsare da ni, idan kuma suka koma ga Sarki Muhammad farsi za su sanar da shi labarin cewar kai ne ummul'aba'isin hana ruwa gudu kamar yadda Yarima Salman ya sanar da shi cewar kun siye duk wani mai zaben Sarki a majalisa kun basu dukiya don su zabi Sarki Hilal maimakon zababben Salman". Koda jin wannan batu sai hankalin Waziri Adnan y abaci ya tunzura wani gumi ya fara taso masa. Don haka sai ya fadi a fusace a mayar da Jarumi Umar cikin kurkuku da ya fito kai tsaye yayi sirri da dakarun don su yi binciken gidan kaf domin neman wasu baki da ba a san kosu waye ba. Sai da aka kusan yini har yammaci ana wannan kewayen ba a samu su Dawan ba, aka zo aka sanar da Waziri hankalinsa ya kara tashi, don haka sai ya tashi dan aike kai tsaye zuwa ga waziri Ja'far domin ya tabbatar masa da halin da ake ciki. Lokacin da Waziri Adnan ya koma majalisinsa ya kasa sanarwa da Tsuffin fada abin da ke faruwa saboda dama yana kan kara basu Karfin giwa akan zabar Sarki Hilal, don haka sai ya sallame su ya ci gaba da nazari da safa da marwa yana cikin wannan lamarin sai uwar Yarima Hilal ta fado masa a rai ita kadai ce zata samarwa da lamarin mafita saboda tafi danta son ya zama Sarki saboda tana tsoron Salman akan irin yadda ta ci zarafin mahaifiyarsa bature 47 Page da yadda ta yi sanadiyar barinta duniya, wadda ta san cewar matukar Salman yah au kan karagar mulki sai ya daukarwa mahaifiyarsa fansa. A dakin gani suka hadu wani daki ne dake mararrabar fadar Sarki da cikin bangaren mata wacce idan ana zaman fada aka so matan Sarki su ji abin da ke faruwa suna iya hawa sama suna hango mutane amma mutane basa hango su, saboda wasu raga raga a can sama sannan suna jin duk abin da ke faruwa, haka dakin Gani yake a kasa idan wani mai mulki ko wani dan aike ko mahaifin Sarauniya ya zo wajen diyarsa idan za su gana suna amfani da wannan dakin gani ne, babu kowaye kai idan ka zo daki ne guda biyu wanda aka tsaga raga raga a haka za ku gana da ‘ya'yan Sarki ko wasu masu aiki a gidan Sarki ba a yadda a hadu fuska da fuska ba, sannan za ka yi kasa da kanka ko ta cikin ragar baka isa ka hada ido da matar Sarki ba. da = har zuwan Sarauniya Ruma, koda ta iso bai bata lokaci ba ya zayyane mata duk halin da ake ciki, hatta dan sakon da ya tasa zuwa wajen waziri Ja'far ya sanar mata. Koda ya zo karshe sai ta ce "Lallai muna cikin tashin hankali, amma duk da haka ka yi abu mai kyau, abin da nake so mu yi yanzu, lallai shi ne ka samu Yarima Hilal ka sanar da shi, cewar shi wannan dan aikin dan leken asiri ne ba wai aikoshi a ka yi ba, saboda ya bada damar kashe shi, idan mun kashe shi, batare da Sarki mai jiran gado ya san cewar dan aike ne daga fadar Sarki Muhammad farsi, ina maitabbatar maka har yanzu akwai shakka da tsoro a zuciyar Hilal, saboda haka kada mu bari ya ji wani labara Sarki Muhammad farsi don zai iya tsorata ya hakura da wannan mulki saboda tsoron mutuwa, idan kuwa muka kashe bakon nan babu wani abu da zai biyo baya koda ya biyo za mu sanar da Sarki Muhammad farsi cewar cewa yayi damu shi dan aike ne daga Yarima Salman. A nan Waziri ya kasance bature 48 Page Koda jin wannan shawara da sarauniya Ruma ta bada sai Waziri ya samu kansa yana mai cikin farin ciki domin lokaci guda ta fitar
🏠