NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 16 of 42

ole mu yi aikin da hikima". Suka shiru suka zurfafa cikin tunani domin gano abin da dan uwansa ya hango a nan gaba. Ko da suka samu dan takin lokaci suna wannan nazari sai Mu'az ya ce "Hikimar ka muke jira ya kai gwarzon Karni domin ka san dai duk abin da za mu ce naka shi ne mafita, domin ban hango wata dabara da za mu yi wajen shiga birnin Shamnum batare da mu samu matsala ba". Jarumi Jarumi Umar ya dubi kowa daya bayan daya domin tunanin ko akwai mai Magana duk kowa ya girgiza alamar ba shi da cewa sai da ya je kai Dawan sai Dawan yace "Mu'az shi ne mafi hikima baya kai tun da har ya baka damar naka nazari ba mu da wani abin cewa don haka muna saurarenka". Jarumi Jarumi Umar ya dauki wani kara dake gefan kafarsa yace “Ni ma bani da wata dabara, ta shiga gidan Sarauta har mu gaña da Sarki sai hanya daya, hanyar daya ce dole a cikin mu za mu rarrabu kashi biyar kowa yayi na shi kokarin duk wadda ya sha a kokarin shiga gidan Sarauta to shi ne zai fanshe wanda aka kama in kuma mun shiga dukkanin mu, to hakan shi ne fatan mu, Mu'az ka bature 43 Page tafi izuwa gidan Sarauta a matsayin dan aike daga bakin Mahaifina, kai ma Dawan, Kai ma Saklahu, kai ma Kubait, kowa zai tafi da ma'ana daban, idan Mu'az ya je bakin kofa in fadawa sun tutsiye shi zai ce da su matafiyi ne shi daga Kasuwar ASSUK, ya zo ne domin tallata hajjarsa ga sabon Sarki, saboda kaji labarin za a yi rantsuwar don haka ka zo da bayanin siya da siyarwa ga Sarki. Dawan kai kuma in ka is aka sanar da su cewar Manomi ne kai da ka zo daga Zurkul domin kawo tallafin kayan noma ga Sarki za ka je fada domin neman yaddar Sarki don gabato da kyautarka a ranar bikin nadin Sarauta. Kubait ka je a matsayin Malamin da zaka nemi yaddar Sarki na yin wa'azi a ranar bikin sarauta, Saklahul kai kuma za ka je a matsayin dan aike daga Birnin Bahara zuwa ga Sarki ka tubure sako ne da kai da za ka kaiwa Sarki, ku tabbatar kun rike wannan dabarar duk wadda ya samu nasarar koda an kama mu to tabbas shi zai fanshe mu domin dolen Sarki ya gaza aiwatar da komai matukar in ya ji da kunnensa cewar Sarki Muhammad farsi ya san da zuwanmu" Da wanan shawara suka tasamma cikin birnin kai tsaye ba tare da bata lokaci ba kowa ya waste ya nufi gidan gadan-gadan gari guda, masarautar Shamnun tsohuwar masarauta ce da wani hamshakin takadirin Sarki yayi mulki a shekaru dari da suka shude, shi ya samar da masarautar tana da girman gaske don a wancan lokaci a cikin masarautar dukka jama'a birnin suke, saboda girmanta, a nan gidaje da kasuwannin birnin suke, sai da duniya ta kara fadi aka samu jama'a da baki da dama, sannan ne aka samar da wasu sasssa a cikin birnin. Saboda haka yanzu idan ka ga wani a gidan to attajiri ne ko mai mulki a kasar, amma duk talakawan gari da baki an tanadar musu waje a waje. Babban gida ne ko na ce bature 44 Page Lokacin da Mu'az ya isa kamar yadda Jarumi Umar ya Jarumi Umarce shi hakaya sanar da masu gadin wajen amma sai suka nuna sam ba zai shiga ba, haka Dawan da sauran abokansa. Duk Jarumi Umar na gefe yana kallon su, sai da ya tabbataṛ duk basu samu nasarar shiga ba sai ya matso kusa da masu tsaron kofar birnin da nufin shiga sai suka dakatar da shi “Kai ina za je?” Jarumi Umar yayi shiru daga farko, sai da mai tambayar ya kara maimaita tambayarsa sannan ya ce "Dan aike ne ni daga Salman zuwa ga Sarki Hilal?” Koda ji haka sai dakarun da suke tsaitsaye a bakin kofar suka tsare shi da dogayen masu suna masu huci da kokarin sukar sa". "Ka ce mene ne?" “Ina so ku kai ne gaban Sarki domin ina da sako daga dan uwansa?" Dawan Kubait da sauran abokan tafiyarsa da suka ga an tsare shugabansu da masu sai hankalinsu ya tashi suka yi niyar cire makamin jikinsu, sai ya daga hannu daga nesan suka fuskanci abin da yake nufi suka fasa aniyarsu. Shugaban Dakarun ya ce "Mazak u rufe shi a kurkuku, ku ci gaba da tsaro ni kuma zan je na sanar da Waziri halin da ake ciki". "Ba wajen Waziri aka aiko ni ba wajen Sarki Hilal aka aiko kuma ina da sako ne daga Sarki Muhammad farsi, zuwa gare shi, yin ganganci da rayuwata tamkar yin ganganci ne ga rayuwar masarautar Shamnun, don haka kai tsaye ku kai ne ga Sarki". Shugaban Dakaru ya daka masa tsawa ya ce "Babu wani wadda zai zo da sako makamancin wannan a bar shi ya shiga ya gana da Sarki kai tsaye lallai sai dai waziri don haka za mu tsare ka aka jira har Waziri ya bada Jarumi Umarni, saboda haka ku tafi da shin i kuma ina nan zuwa”. bature 45 Page A haka aka tsare Jarumi Jarumi Umar Shugaban dakarun da wasu masu dakaru biyu suka bi bayansa zuwa ga Fadar Waziri. Hankalin abokan tafiyarsa ya tashi ainun suka rasa inda ke musu dadi illa Mu'az ne kadai babu wani damuwaa tare da shi, daga bisani ya ce "Ku kwantar da hankali, tabbas Jarumi Umar yana sane da abin da yake yayi hake ne don a hana mu shiga, shi yasan yadda zai shiga ciki, domin idan da bai yi haka ba duk ba za mu shiga ba, kuma za a ka ma mu hakan da yayi akwai hikima
🏠