ka yi musu
alkawarin ci gaba da zama a majalisa, batare da yi musu wani sharri
da kagen da za a kore su daga kan karagarsu ba.
A dai-dai wannan lokacin Sarki ya katse shi yana mai cewa
"Ko Waziri ja'afar yana da wani sani dangane da Gimbiya Suhaila
bin Ababakari?"
Waziri Ja'afar ya amsa "Ina da shi ya Sarkin duniya”.
Sarki ya nuna inda ake tsayuwa a yi bayani don Wazirin ya
fito yayi bayanin kare kai. Batare da bata lokaci ba ya fito ya tsaya a
gaban Sarki nesa da juna inda kowa zai saurare shi ya ce "Daga
birnin Shamnun sako ya zo gare ni cewar Gimbiya Suhaila bin
Ababakari ta gudu daga masarautar Shamnun, saboda haka Sarki mai
jiran gado Hilal maijiran gado ya bada Jarumi Umarni a kamo ta duk
inda take, wannan labari ya iso min daga masarautar Shamnun cewar
an nemi Gimbiya an rasa, dalili ke nan da na ji labarin cewar an
bature
40 Page
ganta a wajen Hakimi Abdullahi bin Sharjas, shi ne bai yi kasa a
gwiwa ba na isa wajensa domin na gasgata”.
Yadda Waziri ke maganar cikin ladabi da nuna tsantsar
gaskiyarsa.
Sarki Muhammad farsi ya jinjina sannan ya dubi Abdullahi
bin Sharjas ya ce “Kaji bayaninsa, kuma shine na wakilta game da
masarautar Shamnun, ka ga yana da ikon sanin komai”.
Da Sarki ya gama wannan jawabin sai ya kara duba ga Waziri
Ja'far ya ce "Me yasa Salman ya gudu ya bar Shamnun, me yasa
Gimbiya Suhaila bin Ababakari tashiga hannun Arnan, me yasa baka
zo min da labarin yanayin da birnin Shamnun ke ciki ba domin a
yiwa 'ya'yan Sarki Sulhu?"
Waziri Ja'afar ya hadiye wani yawo yace "Amsar farko
Yarima Salman bashi da rinjiya a majalisar zabin Sarki, shi ne dalilin
da yasa ya gudu saboda an same shi da bada dukiya ga wasu masu
zabar Sarki, har sun fito sun bayyana, wadda hakan yana nuni da
cewar kai tsaye kisa kai ne domi ya saba dokar masarauta, amsa ta
biyu Gimbiya Suhaila bin Ababakari, eh Yarima Salman ya tura
mata da sako ta barauniyar hanya domin ta gudo ta je gare shi,
domin yana tsoron kada a hallaka ‘yar uwarsa, Yarima Salman yana
tare da Kafiri Jaremi bincike ya nuna mana cewar kafiran da suka
dauko ta za su kaita birnin Hairam, domin su haddasa yaki a tsakanin
yayan Sarki biyu ta wannan damar kuma za su yi amfani da hakan
wajen fuskantar matsaloli a yankin musulmai, dalili na uku kuma
jiya na dawo daga birnin Shamnun ina son a zaman da za a yi yau na
kawo maka bayanin duk da ya faru ya Sarki mai daraja.
Bayan waziri ya gama gabato da labarinsa sai ya juya ya dubi
Abdullahi bin Sharjas daga nan ya bawa Waziri dama ya koma ya
tsaya.
bature
41 Page
Sarki yayi kusan dakika uku batare da ya ce wani abu ba, sai
daga bisani ya dago kai ya dubi dansa Abbas da Zaid ya ce "Zaid ka
tafi da dakarun sulhu zuwa birnin Haiman don fuskantar Benjamin a
game da dalilin dauko gimbiya Suhaila bin Ababakari kai kuma
Abbas na baka aikin bincike da tabbatar da gaskiya a birnin
Shamnun, Waziri zai kasance da mu a nan saboda fuskantar wasu
matsaloli, ina maka fatan nasara a farkon ayyukanka a masauta a
yau.
Da yarima Abbas ya ji wannan batu sai ya duka kansa kasa
cikin girmamawa ya ce "Amin Baba, kuma da yardar Allah zai yi
duk wani abu da zai gamsar da kai da kuma fitar da masarautarka
kunya bisa tafarkin shugaban mu Annabi Muhammad farsiu
Sallallahu alayye wassalam"
Zaid shi maya dukar da kai cikin girmamawa ya ce “Insha
Allahu komai zai tafi kamar yadda ka Jarumi Umarta".
Sarki ya amsa a cikinsa gami da ci gaba da batu "Hakimi
Abdullahi bin Sharjas, ka yi namijin kokari kuma a jinjinawa Jarumi
Umar a gaya masa muna alfahari da shi bisa kokarinsa na ceto yar
musulmi kuma Gimbiya daga gobar kafurai, sannan muna maka
maraba da zuwa babban birni don shigo da abin da ya shige maka
duhu, za mu yi aiki kai da fata wajen magance dukkanin abubuwan
da za su kawo mana ci gaban kasarmu da musulunci".
Daga nan Sarki ya nemi wani mai Karin bayani kowa yayi
shiru bai ce ta tafasa ba haka ya tabbatar da cewa ba wani korafi don
haka Zaman majalisa ya tashi".
**
A tsakanin dagawa rana zuwa kwallewarta suka isa cikin
birnin Shamnun, sun yi gudu da dawakai ba tare da yada zango ba,
sun isa birnin dai-dai da lokacin da ake kiraye kirayen sallar la'asar
don haka sai suka yada zangon farko a bakin garin kusa da wata
bature
42 Page
rijiya daga gefe ga wani gini nan na saukar baki akwai masallaci a
wajen.
Lokacin sallar ya riga ya kure shi yasa basu bata lokacin hutu
ba suka yi sallar laʼasar sannan ne kuma suka fara tunanin abin da ya
dace ayi. A dai-dai wannan lokacin ne suna zaune a bakin ganuwar
birnin Shamnum suna hutawa tare da cin abubuwan don cika cikinsu.
Jarumi Umar ya nisa ya dubi abokan tafiyarsa ya ce "Da
akwai alamun tsaro a birnin nan mai tsauri, kuma ina kyautata zaton
maganar mahaifina ta tabbata sakon zuwan mu ya riga mu kara sowa,
yanzu dole mu sake shiri domin muka ce za mu tafi gaba gadi tabbas
za su yi galaba akan mu a ka ma mu a rufe ko a hallaka a saka mu a
lissafin masu goyan bayan rikicin masarauta don haka d