na bukatar birnin nasa wadda aka kwace masa Birnin
Hilayan, sanan yana bukatar diya ta rayuwakan da aka salwantar a
birnin yayin gwabza yaki, ya kara tabbatarwa ba zai kara turo sako
na hudu ba, kaifin takobi ne zai ci gaba da Magana.
A bagaren Kauyen Dire Hakimi Suleman yayi batu a game da
bullowar Hangalawa tsille tsille suna zuwa babbar kasuwar Kudu
suna tare mutane suna kuma zuwa suna amsar haraji, lallai yana mai
kira da babbar masarauta a dauki lamarin da gaske domin sun fara
dawowa.
A ziyarar da Waziri ya kai kasuwa jiya, ya ci karo da sabbin
mutane wadda ya sa an yi bincike a kansu ya gano cewar lallai wasu
bature
37 Page
mutane ne da suke son haddasa husuma domin sun dauko 'yar
marigayi Sarki Ababakari zuwa wannan birnin amma cikin ikon
Allah Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya kwace ta daga hannunsu.
yau".
Wannan su ne bakin labarin da za mu fito da su a zauren mu
Fada ta kara yin shiru bayan da Zirkifilu ya kammala kawo
batutuwa kamar kullum. Sarki ya gyara zamansa kai tsaye
idanuwansa ya dago ya dubi kafatannin ‘yan zaman fada kafın ya
dora ya ce "Sako zuwa ga Kafiri Jarman Jakub a gaya masa cewar ba
mu da lokacin mai kori, ba kuma da wata Magana da ta rage a
tsakanin mu, idan har ya tabbatar Takobin ce kadai za ta yi Magana,
to na mu kodayaushe cikin washi suke.
Game da Hakimi Suleman lallai a tashi dakaru na gaske a je
Kauyen a yi bincike na gaske.
Kafin Sarki ya kara Magana ta gaba, sai ga Shugaban Fada ya
shigo tun daga nesa ya duka yayi gaisuwa "Akwai sako na
musamman ya Sarki mai daraja”.
Tun da Waziri ya ga shigowar Sarkin Fada sai hankalinsa ya
ta shi, ya shiga zare idanu amma tun da dai yay i aikin hankali tun a
jiya ya shigar da batun kafurai a kasuwa karyar da zai yi za a iya
gasgata ta, maganar Salman ce wajen binciko lamari wannan kuma
ya san shi zai jagoranci zuwa birnin kuma ko ma waye a cikin fadar
to maganarsa yake ji.
Har Sarki Fada ya je kusa da Sarki yayi masa Magana da ba
kowa ne ya ji ba. Ya bawa Sarkin Fada Jarumi Umarni ya fice "Batu
a kan Yar Sarki Ababakari ga Hakimi Abdullahi bin Sharjas nan ya
iso domin yi mana cikakken bayani".
Kowa da ke wajen sai da gabansa ya fadi domin koda wasa
aka furta sunan Abdullahi bin Sharjas sai mutane sun shiga
hankalinsu sun fara tunanin wata badakalar ta su za ta iya ta shi,
bature
:
| Page
saboda tsoronsa da kuma, Sarki na rufe baki Abdullahi bin Sharjas ya
bayyana cikin sallama bangaren ya tsaya cak yana kallon kowa cikin
fara'a.
"Bangaren Masarauta, Malamai, Hakimai 'yan uwana dakatai
Wazirin ina muku sallama ta addini musulunci".
Kowa ya amsa masa sannan ya nemi wajen tsayuwa ya tsaya
a sahon Hakimai.
Bayan yin shiru na dan lokaci sai Sarki yayi gyara murya ya
ce "Abdullahi bin Sharjas, sako ya zo daga Wazirin Bahara cewa ka
kubutar da 'yar Sarki Ababakari daga hannun kafura, z aka iya
fitowa ka yi mana Karin bayani”.
Abdullahi bin Sharjas ya fito daga inda yake tsaye ya tsaya y
ace "Tabbas da na Jarumi Umar shi ne ya tare su ya kuma amso ta ita
da wanda yake yi mata hidima, sannan bayan haka Waziri ya zo har
Kauye nemanta da yunkurin a bashi ita. Gimbiya Suhaila bin
Ababakari ta sanar da mu cewar Dan Sarki Salman ya saye duk wani
Dakare, da duk wani dan majalisar Sarki shi da mahaifiyarsa, na
lalllai shi ne zai gaji Sarautar mahaifinsa, a yanzu haka ma ranar
rantsuwa kadai ake jira domin shi yake gudanar da komai, sannan ta
ce ya bazama nemo dan uwansa Hilal. Shi kuma Yarima Hilal shi ne
yay i sako ga 'yar uwarsa cewar ta gudo daga birnin a kokarinta na
guduwa suka kama ta kuma suka tilastata akan sai ta kai su ga inda
Yarima yake, dakarun da suke tare da ita kafurai ne, kuma sun nufi,
Birnin Bahara da ita, wannan dalilin yasa na ce ya dace na zo kada
da kafa domin jin ba'asi ko sakacin da Sarki ya jima yana yi ya fara
taba martabar Sarautar Bahara"
x
Wata tsawa Shugaban Dakaru da Waziri suka dakawa
Abdullahi bin Sharjas, har da zare takubba. Sarki ya daga musu
hannu alamun su dakata cikin tsawa. Shi kuwa ko gezau bai yi ba
bature
B
38
39 Page
domin bait aba zuwa fada bai furta Kalmar sakacin nan ba, ba kuma
su fasa kawo masa bar aba, sarki bai fasa dakatar da su ba
"Muna bukatar ji daga gare ku, sannan kada ka manta Waziri
Ja'far sa'a daya da kawo Suhaila bin Ababakari wajena ya biyo
sahunta, shin me ya sani dangane da zuwanta, dole sai an sarewa
maciji kai kafin a samu nutsuwa"
Koda Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya zo nan a batunsa sai
yayi shiru ya kuma koma ya tsaya jin ta bakin Sarki Muhammad
farsi.
Lokacin Sarki Muhammad farsi yayi dakika biyu yana nazari
kafin ya ce wani abu, a wannan lokaci shi ma Waziri Ja'afar yana na
shi nazarin da ya kwana yana maimaita amsar da zata fitar da shi
daga zargi, don haka tun da dan aikin Shamsu bin Aujarya zo masa
yayi tashi dan aiki zuwa masarautar Shamnun abu na farko ya
gargadi 'yan majalisar masu zabar Sarki saboda su ne wadanda aka
tilasta su, aka kuma cika musu aljihu da sulalla, sannan a