NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 13 of 42

a shiga turakarsa duk wani abin bukatarsa ya dauko ya fito, bai tsaya ko in aba sai wajen abokansa, da sun yi shiri tafiya. A dai-dai lokacin da suka haye dawakai sai suka rufarwa hanya babu ji babu gani. A daidai wannan Lokacin Shamsu bin Aujarbn Abdallahi ya na hangensa daga can saman gidansa koda ya bature (. > 34 Page ga sun fita sai yayi sauri ya sakko ya nufi cikin gidan dan sanin abin da yake faruwa. A lokacin da Sarki Abdullahi bin Sharjas ya gama kintsawa sun fito tare da matarsa da kuma Gimbiya Suhaila bin Ababakari da Jarumi Ahmad. A hankali ya matsa gare shi jiki a sanyaye. “Dan uwana naga Da na Jarumi Umar tare da abokan gumurzunsa sun sukwani dawakai, kai kuma ka fito cikin shiri shin akwai wani abu ne da ba mu sani ba”. Hakimi yayi murmushi ya ce "Kwantar da hankalinka yanzu nake shiri na shigo Bangarenka na zayyana maka abin da ke faruwa, sai kuma g aka, Amanar mutane na iyalina, da gari na na hannunka, domin wata tafiya ce wacce ba a kimtsa mata ba ta same mu, dole daga yanzu za mu wuce Bahara, zan gana da Sarki akan matsalar gimbiya Suhaila bin Ababakari, sannan Jarumi Umar da ka gani ya fita shi ma ya tafi Shamnun ne domin magance matsalar da ikon Allah zuwa yammaci za mu dawo" Koda Shamsu bin Aujarya ji wannan batu sai yayi shiru da ya fuskanci shirun nasa zai kawo wani tunani daga dan uwansa sai ya ce "To Allah ya dawo da ku lafiya, kuma za mu ci gaba da gudanar da tafiyar komai har Allah ya dawo da kai lafiya". ya Daga nan ya bi su da kallo suka dunguma kusan dakaru ashirin ne ke musu rakiya. Bai gushe ba yana kallonsu har sai da suka bace masa da gani sannan yayi sauri ya nufi gida, ya sa a kira wo masa babban yaron sa Alban koda zuwa Alban sai dube shi ya ce "Maza ka je ka tashi ka je ka isar da dan aikin Waziri cewar lallai dan uwana ya yi abin da yake zargi wato ya nufi Bahara, shi kuma Jarumi Umar ya nufi kasar SHamnun, ka yi maza ka da ka bata lokaci". Alban ya fita da hanzarinsa don kai sakon maigidansa abin sirrinsa gatan sa kuma. bature B 35 Page Shamsudden wani mashahurin tsoho ne wadda yake adawa da mulkin dan uwansa, bai yi amana da Abdullahi bin Sharjas ba domin gani yake shi ne mafi cancanta da sarautar Annur, don haka kullum cikin bakin ciki da zagon kasa yake yiwa Mulkin Abdullahi bin Sharjas tsawon shekaru bai taba samun nasara ba, Abdullahi bin Sharjas ya sha kama shi da hada baki da wasu maha'inta kasa amma yana masa afuwa, saboda son a zauna lafiya domin abin da Abdullahi bin Sharjas yake fadi kullum shi ne dukkaninsu sun zama dattijai lokacinsu kalilan ne a duniya, baya son dan uwansa ya mutu a matsayin mai ha’intar kasa, kullum yana gyara masa kurakurensa, amma ya gaza fahimta, don haka duk lokacin da ake so a cimma wata manufa a cikin kauyen Annur to da shi ake hada baki, don a jiya da waziri ya bar kauyen sai ya sa dan aike zuwa gareshi ya sanar da shi cewar yana bukatar jin duk wani motsi da ya ga dan uwansa yayi. Tun da Waziri Ja'afar ya bar Kauyen Annur bai tsaya ko ina ba sai gidansa a babban birni saboda ya san cewar za a samu wannan babbar matsalar, don haka washe gari da sassafe ya zo fada don ya yi tsarin da zai warware kansa daga cikin matsalar birnin Shamnun kafin a samu wata matsala Ana zaune a fada kowa ya iso isowa Sarki Muhammad farsi kawai ake yi. Wasu da dama a fadar sukan tattauna batutuwan da suka zo wa da Sarki shi na yadda za su sanar da shi, wasu kuma na kokarin gyara Kujerar Sarki wasu na gyatta tsayuwarsu, malamai wasu daga cikin Hakimai da aka gayyata, Sarkin Kasuwa, Sarkin gida, da na fada Shugaban Dakarun waje da na Gida duk sun hallara suna jiran Sarki. Kwatsam sai ga Busar Sarewa alamar Sarki ya taho, ‘ya'yansa biyu ne suka fara shigowa cikin takama da nuna izzar mulki wato Yazid da Abbas. A nan take kowa ya mike a fadar aka bature ミ 36 Page fara dukar da kai kasa ana gaida su. Sai da suka nemi wajen zama sannan ne kowa ya zauna kuma waje yayi shiru. Jim kadai sai ga Sarki nan shi ma nan aka kara tashi yana tafe wasu dakaru biyu suna biye da shi kansa a kasa yake har ya isa inda kujerar mulki take wadan an dakaru suka koma hagu da dama suka tsaya a bayan kujera sai ya dago kai ya dubi duk inda mutane suke sannan ya daga hannu ya fara addu'a domin fara zaman majalisa, a ka yi salati ga manzon rahma, aka yi kirari ga ubangijin talikai aka nemi taimakonsa da goyan bayansa a game da daukaka Kalmarsa. Sannan aka shafa da fatiha. A sannan ne ya nemi waje ya zauna. To fa babu mai zama a wannan wajen har a tashi taro a haka kowa zai tsaya. Mai rubutun kundin mulki da kuma gabatar da abin da za a fara jira yake Sarki ya daga masa hannu ya fara domin dole shi ne farko adaidai lokacin Sarki ya daga hannunsa sai wannan mutumin da ake cewa da shi Zarkifilu ya fito gaban Sarki da katon kundinsa a hannu ya fara da cewa "Allah ya ja zamani Sarki ya karawa Sarki lafiya kamar kullum da kodayaushe, batu daga Sarki Jarumun Jakub cewa a karo na biyu ya
🏠