NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 11 of 42

rninsa amma dole tasa ya tsaya saboda a kowane lokaci ana koyar da su da su bi musulmi domin su samo lagon da za su kama su da sasari.' bature Data 28 Page su kashe shi shi ne ya sa a wannan lokacin ba ni da wani sukuni tun da Sarki ya fara ciwo yau gobe lafiya gabana ki faduwa". Hindu ta yi shiru cikin dan gajeren lokaci har sai da ta ji uwar dakin nata ta share hawayen ta ja shessheka sannan ta ce "Neman taimakon Hakimin Annur daidai ne a gare ki, domin shi mutum ne adali kuma mai matukar son gaskiya, idan Allah zai baka kariya ba da kansa zai zo ya baka kariya ba, amma shi ne zai zama sanadin haka, kin fi ni sani duk wani ilimi a wajen kin a samo shi, tsantsaini da tsoron fadawa halaka yake sawa kike wannan tunanin ai saka miki damuwar da kuma tunanin nemo wadda zai tsayawa danki ki dauka ubangiji ne yake haska miki, a da can ban da karfin gwiwa a game da Yarima Abbas amma wannan maganar take ta sa na fara jin karfin gwiwa, tabbas mu yi hanzari ka da mu yi kasa a gwiwa”. "Maganar ki gaskiya ce, wannan haka yake, to amma yake Hindu ya kike gani za mu yi wajen ganawa da Hakimi Abdullahi bin SHarjasllah, ki sani cewar matukar sun san wani shiri to za su gyara na su shirin, abin da nake tunani wani amintacce za ki nemo min wadda zai kai masa ziyara wadda shi da kansa Hakimi zai nemi yarima ni kuma zan gayawa yarima sakon da zai je masa da shi”. ** Lokacin da Jarumi Umar ya iso babban turakar mahaifinsa, a daidai lokacin Hakimi na nazari game da bakuwar Suhaila bin Ababakari da kuma tunanin sakon da Sarauniya Hauletu ta zo masa da shi na son haduwa da Yarima Abbas. A wannan lokacin ya yanke kai ziyara babban birnin domin ganawa ta musamman da Sarki a game da sabuwar masarautar da ake rigima a kai, sannan kuma zai yi amfani da wannan dama ya gana Yarima Abbas. da 29 | Page Ya dubi 'ya'yansa biyu da suke durkushea gabansa ya fara da cewa "Ya kai Ahmad ina son kasani za mu yi tafiya a safiyar yau zuwa birnin Bahara, kai za ka yi min rakiya zuwa can". Ya dubi Yarima Jarumi Umar da yake a tsorace daga furucin Hakimi, domin idan akwai abin da yaki jini ya ji ko gani mahaifinaa y acc zai yi tafiya ba tare da shi ba. "Ya mai martaba ka yi sani cewa zuciyata tana shiga rudani hankalina baya kwanciya a duk lokacin da na ji cewa za ka fita daga cikin wannan kauye, Ya mahaifina ka sani cewar makiyan da suke son ganin bayanka a kasar nan sun fi makiyan waje yawa, idan har za ka kai...." Hakimi ya dakatar da shi da cewa "Ka kwantar da hankalinka Jarumi Umar, ka sani cewa wani muhimmin aiki ne ya taso wadda kuma yana bukatar na motsa, kai ma kumana tura ka wani aiki na daban aikin suna bukatar a yi su a tare domin dole ne na je na gana da Sarki Muhammad farsi dangane da matsalar Salman da Hilal, dole kai ne zaka tafi izuwa kasar Shamnun domin ka gano mana halin da ake ciki" Ran Ahmad ya baci ya dubi Jarumi Umar ya cc "Akowane lokaci kana jin cewar kai kadai ne kariya ga ahalin gidan nan, idan har ba zan iya kare mahaifina ba, na tabbata ba zai yanke shawarar tafiya da ni ba". Jarumi Umar ya girgiza kai yace "Ba haka nake nufi ba dan uwana, babu mai kare wa face ubangijin musulunci, abin da nake tsoro da fargaba shi ne buguwar zuciya yayin da na tuno kuna halin tunkarar birnin da yake cushe da makiyanmu, masu son ganin bayan mahaifinmu da ahlinsa". Hakimi yayi murmushi ya dubi Ahmad y ace "Iya abin da dan uwanka ya fada shi ne kadai abin da yake gudu, amma ba ya nufin cewar kai ba zaka iya bani kariya ba." bature 30 Page Sannan ya dubi Yarima Jarumi Umar ya ce "Aikin dake gabanka ya fi wanda ke gaban mu hadari, dole sai kun yi kaffa kaffa domin na san za a zuba dakarun da zasu hana ku ganawa da Sarki Hilal, domin ba bukatarsu a yi sasanci ba bukatarsu ayi tashin hankali a tsakanin kasashen musulmai, amma a zarar kayi tozali da Sarki Hilal ka yi masa albishir da cewa na tafi zuwa babban Birni don tabbatar da cewar shin Sarki ya san da abin da yake faruwa a kasar Shamnun ko kuma bai sani ba, wannan kalamin shi ne kadai zai sa Sarki Hilalya barku ku dawo gida lafiya, kuma idan yana da hankali shi zai sa a barwa duniyar musulunci zabar Sarki mafi daraja a tsakaninsu shi da dan uwansa Salman, amma matukar basu gan ku kun gana ba, to ku yi kokari tsirar da rayuwarku domin sun shirya ayi duk abin da za a yi, ka ga ke nan za su fara da kai”. Jarumi Jarumi Umar ya jinjina kai ya kuma fuskanci lallai akwai babban aiki a gabansu,don haka ya jinjina kai ya ce “Insha Allahu komai zai tafi kamar yadda ka tsara Baba". Hakimiya jinjina kai gami da cewa "Masha Allahu, yanzu ka je ka yi shiri tun da har yanzu muna cikin duku-dukun safiya, don haka idan kun tafi yanzu kafin la'asar za ku isa birnin Shamnun, kuma lokacin mun fara neman hanyar dawowa daga Birni, duk ku tashi ku je ku yi shiri". Ahmad da Jarumi Umar suka fito daga babbar turakar mahaifinsu cikin fushi da Ahmad yake ciki da dan uwansa domin shi sam gani yake kanin nasa ya raina masa t
🏠