NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 9 of 22

a ce, "Na'am' " Ta matso kusa da shi har sunajin numfashin juna, ta saisaita muryarta tana wasa da zagayayyen gashin bakinsa ta ce, "Alhajina wai ni lafiya? Duk fa 'yan kwanakin nan haka kake kafiya yawan shiru da tunani. " 53 IZGILL JAMILA MUHAMMED Ya sauke ajiyar zuciya ya ce, "Akan dai zancan nan da mu ka yi dake ne kwanaki, to wallahi yanzu abin ya dame ni sosai so nake in zaɓa masa kawai sai dai ince masa rana kaza dan nagaji da wannan shashancin banzar da yake yi. Dai dai nan wayarsa dake gefensa ta ɗauki ringin yana duba wayar yaga my son ya ce, “Kin ganshi ma ya danna ok ya fara maganar sosai da suka dan daɗe sannan ya mikawa mominsa tana yi masa fadan yaki zuwa ko ya makale Abuja. Ya ce, "Aiyuka ne Momi su kai min yawa amma insha Allahu zan zo karshen wannan satin. Ta ce, "Ka dai faɗa ne. 99 Sun dade suna magana sannan ta kashe wayar ta dubi Alhajin ta ce, "Dan Allah Alhaji ka sassautawa ranka ka daina yawan tunanin nan kar wani ciwo 54 IZGILI JAMILA MUHAMMED ya kamaka kabi komai a hankali dan Allah. Ya yi dariya ya ce, "To ranki ya dade za'a yi yanda kike so gaba daya suka yi dariya." NIGHT CLUB Club din cike yake makil da ‘yan kosassun Abuja ‘ya'yan manya Club din yai mutukar tsaruwa tamkar a turai, zaka yi mamaki ainun da man akwai club kamar wannan a Nigeria saboda yadda ake zuba lalata tamkar a garin nasara, asarar duniya babu abinda ketashi sai wani tattausan Music mai ratsa kwanya kowa sai harkokinsa yake kwanciyar hankali wasu gurin shaye shayensu su kafi kauri yayinda wasu gurin rawa suka karkata dai-dai nan Hisham Mansir kwangila ya baiyana gaba ɗaya samarin gurin suka ruɗe da ihu cikin 55 IZGILI JAMILA MUHAMMED wadanda suke kusa suka dinga rungumarsa ya yinda wadanda suke nesa suke yi masa fito suna fadin Hey hand some. Cikin takunsa na kasaita gami da shariya yake ɗaga musu yatsansa biyu bai saurari ko ina ba sai can wata kujera ta musamman yana zama Joh mai aiki gurin ya russuna cikin girmamawa ya ce, "Yallaai barka da zuwa.' Cikin kallon nasa na ka'ida ya kalle shi ya ce, Cikin wata daɗɗan muryarsa "Guiness masu sanyi zaka kawo." " Cikin sauri ya ce, "An gama oga. Ya kishingida ya daga daradaran kyawawan idanunsa yana bin club din da kallo ya ajiye wayoyinsa akan table ya fito da kwalin sigarinshi daga aljihun ya 56 IZGILI JAMILA MUHAMMED mannata abaki ya dauko lighter ya kunna yana bulbular da hayakin. Nan take ya haɗa dan karamin gajimare cikin kwarewa yake fesar da hayakin tun shigowarsa. Hankalin 'yan matan gurin ya yo kansa sai shawagi suke ta gabansa ko da Allah zaisa ya kyasa, kowacce so take taga ta burgeshi tana so ta samu shiga a ce yau ya yi mu'amala da ita koda sau daya ne, dan ta san kudin da zai shaka mata ba kaɗan bane, wasu kuwa so suke ya kula su ko bai basu komai ba, ai abun burgewarsu ne kyakkyawa na bugawa a media kamarsa ya kulasu, to su abin alfaharinsu ne musliki dan wulakancin tabar hannunsa ta fisu daraja, a gurinsa, dan shi ko da zai mutu saboda bukatar mace in ba kin isaba kin kai kin kawo wajen haɗuwa gami da aji ba, to ko kallanki ba zai yi ba, 57 IZGILL JAMILA MUHAMMED balle har ya hada jikinsa da na ki dan shi ko cikin mata ba kowace kwashi kwaraf yake kulawa ba, sai ya tabbatar kina da abin kallon sannan zai kalla shi yasa wasu mazan abokansa suke ce masa ba kai kake kallonsu ba, kai ake kallo. Ya lumshi idansa yana jin wani yanayi mai dadi can idanunsa suka kai filin, rawar nan idansa ya hasko masa wata yarinya sai juyi take mai ban sha’awa ya kura mata ido yana kallanta, sanye take cikin wite yar bingilar riga wadda gaba daya cillyoyinia, awaje suke rigar kuwa bata da hannu gaban rigar anyi mata gidan bireziya mamanta rabi duk a waje, suke tana sanye da wasu dogayen, takalma wanda suka dace dashigart kanta yasha wata mici micin kalaba gashin kanti, fara ce, tas, kunnuwanta sanye da dogayen yari gaba daya ta gama 58 IZGILI JAMILA MUHAMMED tsuma shi ta yanda take sarrafa hips dinta tana takawa cikin aji dai-ɗai nan Joh ya dire masa kwalaban sassanyar agabansa da ya jerosu akaǹ\ wani dan madaidaicin faranti, da kuma wasu kananan kofuna na karau, ya saka opener ya buɗe masa ya zuba masa gami da dan rusunawa ya ce, "Oga ga shi nan." Hisham ya dauko kofin batare da ya dauke idanuwansa a gurinba ya ci gaba da tultulawa tumbinsa ruwan barasar yana wani kasa-kasa da marayun idanuwansa yana kare mata kallo, tamkar ance mata juyo sai ta hango mai tsada sunan da yawancin 'yan matan suke faɗa masa ya wani dalalo mata waɗannan fitinannun idanuwannan nasa. Sai ta ji wani irin matsanancin farin ciki ya kamata ta san ma'anar kallon cak ta tsaya da juyin da " 59 IZGILI JAMILA MUHAMMED take yi kuma ta fito daga filin cikin taku mai jan hankali ta baro gurin rawar. Ta kara so gurinsa tana zuwa taja kujera dake gefensa ta zauna ta ce, cikin harshen turanci ta ce, “Barka da dare hand some cikin kal
🏠