ofar ya ya ɗan
danna mata key ya rungumeta ya cika
46.
IZGILI JAMILA MUHAMMED
hannunsa da albarkatun kirjinta su kai
bedroom dinsa.
Inna Lariya ta shigo dakin da kofin
silba a hannunta ta dire shi gami da zama
ta ce, "Hadiya ki tashi ga fura malam ya
shigo miki da ita."
Hadiya da take kodundune akan
yalolowar katifarta tai magana daga
kudundunen da take tace, "Inna na
koshi."
Inna ta ce, "Ai kuwa baki isa ba kin
taɓa jin inda aka warke daga cuta alhalin
ba ashan magani, ba kuma a cin abinci
saboda tsabar gardama da kafiya irin naki
to tunda nadama furar sai kin shata, idan`
ma zaki samawa kanki lafiya ki ta shi to
ki tashi dan wallahi sai kin sha, kin kuma
sha sha mu gani tunda ga shi an sami
kudi an sayo miki."
47
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Hadiya ta ture abin rufarta ta tashi
zaune ji take kanta tamkar zai tsage
saboda ciwon da yake yi mata ga kuma
matsanancin zazzabi. Ta dauki furar
tunda ta ji Inna ta rantse ta san dole ne ta
shata ta fara sha tana yamutse fuska duk
santa da kaunarta da furar ji ta yi tamkar
maɗaci take sha tana yin kurɓa ɗaya biyu
ta dire kofin ji take tamkar zata yi amai,
Inna ta saka mata manyan idanuwanta ai
babu ariziki ta dauki kofin dan ta san
ma'anar kallon.
Haka ta dinga daurewa tana sha sai
da ta sha rabi sannan ta kalli Innar dan
taga a wana yanayi take, da taga bata
nuna komai ba sai ta a jiye ta ɓare
magungunan ta bata ta karɓa ta ce, “Dake
wata ce, ai da sai ki bari sai maganin da
furar da kika sha sun fada miki sannan ki
kwanta."
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Hadiya ta hadiye maganin nan da
kyar ta dauki mayafinta ta dukunkune a
cikinsa amma bata kwanta ba, dai-dai nan
su ka ji sallama Jana Inna ta dauki kofin
ta fita tana amsa mata sallama.
Jana suka gaisa da Inna, jana tana
tambayar mai jiki Inna ta ce, "Da sauki
tana ciki ki karasa."
meJana ta shiga ɗakin ta zauna ta kalli
Hadiya cikin tausayawa ta ce, "Sannu
Hadiya."
Hadiya ta ce "Yauwa."
Jana ta ce, "Ya jikin naki.?"
Ta ce, "Da sauki.
Jana ta ce, "Iya ta ce, a karayi miki
sannu.'
Hadiya ta ce, "Ina amsawa."
Jana ta ce, "Habib ma yana duba ki
ya ce, ya na miki sannu.'
Ta ce, "Ina amsawa."
49
"
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Haka suka dinga yin hirar yan
makaranta Islamiya da boko da yake duk
ajinsu daya tana gaya mata wadanda suka
ce ai mata sannu, saboda basu sami
damar zuwa dubata ba, dan gaskiya
Hadiya tana da farin jinin mutane da
wuya ta zauna a guri ba a so ta ba, ba dan
komai za a so ta, dan kyanta dan can din din ita
kyakkyawa ce ta ajin farko kuma tana da
san mutane tana da mutukar fara'a in dai
ta sanka in bata sanka bane tana da wuyar
lamari.
Alhaji Mansir ya dauki lemon
Edotic din da mai dakinsa Hajiya Zalifa
ta tsiyaya mai ya kurɓa gami da daukan
remote control ya rage sautin
tangamemiyar T. b plasman dake like
jikin bango girmanta ya shahara tamkar
mutanan jiki zasu fito ya kalli gefensa
IZGILI JAMILA MUHAMMED
inda Hajiya Zalifa take dan kishingiɗe
kan tuntum tana cin Tufa suna kuma ‘yar
hira.
Ta zuba kwalliya tamkar mai zuwa
fadar shugaban kasa, daman gata mai
kyau duk mptsin da tai wani fitinan nan
kamshi ne yake tashi, Alhaji Mansir ya ci
gaba da kallanta. Gaskiya yana san
matarsa yana kaunarta ko dan gayunta
sam bata tsufa tamkar yanzu aka kawo
masa ita gidansa shi yasa yai ta ganin
bakin danginsa da suke damunsa da
zancan aure yanzu sun daina, ya riga
yasan Zalifa ta mallake zuciyarsa babu
sauran gurin da zai saka wata ‘ya mace,
ya san ba zai iya hada daki da wata
macen ba dan yadda yake santa yake san
farin cikinta ba zai so damuwarta ba ita
kuma a duk duniya babu abinda ta tsana
sama da kishiya bata santa kwata-kwata
51
IZGILI JAMILA MUHAMMED
.
tana kishi da abinda take so tana bashi
kulawa sosai tamkar wani jariri haka take
tattalinsa tun a farkon auransu har zuwa
yanzu.
Yau kimanin shekara talatin da
takwas ke nàn da yin aurensu amma bata
taɓa ɓata masa rai ba, tana sani ba, sai dai
a ajizanci irin na dan adam, tana sonsa
tana kyautata masa, tana san 'yan
uwansa, tana kyautata musu, tana sansu.
so na gaskiya, Allah mai hikima ne da ya
ce, muddin mutum yai sa'ar mace ta gari
lallai rabin imaninsa ya cika, sai ya
kyautata aiyukansa, dan ya samu rabauta,
ranar gobe kiyama, gaskiya mace ta gari
jin dadin namijin duniya, mace tagari ita
ce, silar wanzar da zaman lafiya gaba
daya ya shagala da kallonta yana fasalto
abubuwan alkhairinta gaskiya duk iya
zamansa da ita bai taɓa ganin wani abun
52
IZGILI JAMILA MUHAMMED
assha kona Allah wadai data taɓa yiwa
wani, wani abun narashin kyautatawa ko
zamanin da 'yan uwansa da mahaifiyarsa
suka saka mata karan tsana.
Can hajiya Zaliya ta kula da
hankalin Alhajin baya kanta dan sai
magana take yi masa amma hankalinsa
yana wani wajen bai ji ta ba ta dago dan
taga mai ya ke yi sai taga ya zuba mata
ido ashe tun dazu ita yake kallo ta mike
zaune daga kishingiɗar da ta yi ta kira
sunansa, yai saurin sauke ajiyar zuciya y