NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 6 of 22

ta lumshe idanta tana shafa dan gashinta, da gaba daya tattalin arzikinta yake karewa akansa tai wani wal da idanunta ta ce. "Daga wa kuwa? In ba daga Hubbina ba." Hadiya ta ce, "Gaskiya ya burgeki da waya, ana ji da wannan Salim din." Jana ta ce, "Wallahi kuwa ai duk cikin samarina babu wanda nake so kamarsa, wallahi Hadiya in har narasa shi ban san yadda zanyi ba na san sonsa IZGILI JAMILA MUHAMMED mahadin rayuwata ne kin ga in bashi ba babu rayuwa." Nan da nan Idanu Jana suka kawo kwalla ta ci gaba "Har tsoro zuciyata take bani ganin irin son da take masa ina sansa har ban san yadda zan kwatanta miki ba, jiya da ya zo tamkar zai yi kuka yake gaya min babanshi ya zaɓa mata 'yar abokin babansa wallahi tun jiyan har yanzu bana cikin nutsuwa hankalina a tashe yake dan idan narasa shi komai yana iya faruwa." ." masa Sai hawaye ya wanke mata fuska tamkar an bude famfo. Hadiya ta ji waii matsanancin tausayinta ya kamata, ita dai bata san so ba dan bata taɓa jinsa ba amma zama da Jana sarkin soyayya yasa ta fara fahintar so, abu ne mai dadi amma idan an dace kuma mai mutukar hadari idan anyi IZGILI JAMILA MUHAMMED rashin dace ta koma fahintar rabaka da abin son ka ba karamin tashin hankali bane. Ta matsa a hankali ta dafa kafadar Jana da take ta sharɓar kuka ji take tamkar ta tayata, ita ma kwallar ta tarar mata ta dai daure dan kada ta kara dagawa Janar hankali ta ce. "Dan Allah Jana ki dinga daukan lamarin da sauki kuka ko tunani ba zasu yi miki magani ba ki dage da addu'a a yanzu ita ce magani in dai Salim mijin ki ne to fa labudda sai kin aure shi, idan kuma ba mijinki bane Allah yasa hakan shi ne mafi alkhairi kin ji dan Allah Jana ki sassautawa kanki dan kada ki saka kanki a wata matsala. Jana ta ce, "Na ji in Allah ya yarda zan dage da addu'a har mu ga abinda Allah zai yi." t IZGILI JAMILA MUHAMMED Hadiya ta yi dariya ta cc, “Ko ke fa my sister tayi dariya. Ya yi nisa cikin tunaninsa har bai ji abinda uwar gida sarautar matan take fadi ba, ta shafa fuskarsa ta ce, “Wai ni Alhaji me ke damunka kwana biyu, duk ka canjamin kana yawan zama shiru kana dogon tunanin har baka jin me ake cewa dan Allah idan wani abunene yake damunka ka tai maka ka gayamin dan wallahi idan baka gaya min ba ni ma zaka sani a wani hali.” Alhaji Mansir Kwangila ya sauke ajiyar zuciya ya ce, "Babu abinda yake damuna Zalifa kawai dai ina wani ɗan nazari ne amma karki saka komai a ranki." Ta kalle shi kawai sai kuma ta mike da sauri zata bar falon, ya yi saurin IZGILI JAMILA MUHAMMED janyota da karfi ta fado jikinsa please Zalifa baki yarda da abinda nace ba ko, to ki kwantarmin da hankalinki ba wani abin tashin hankali bane amma ba zan gaya miki shi yanzu ba sai dai na miki alkawari da zarar na gama bincike zaki ji komai." Ta yi sauri sauke ajiyar zuciya ta ce, "To Allah ya mu ji alheri.' " Ya ce "Alherin ma za ku ji” Ta ce, "Shi muke fatan ji a duk inda muke" Ya ce, "To yanzu hankalinki sai ya kwanta da har za ai min fushi dan kawai ki sani a uku.” " Ta saki wata irin dariya mai kara mata kyau ta ce, "To Ai ban ji dalilin sauyawartaka ba a 'yan kwanan kin nan ka ga kuwa hankalin nawa bai kwanta ba zai dai kwanta. 37 IZGILI JAMILA MUHAMMED Ya ce, "Tun da na ce zan gaya miki to zan gaya miki da zarar lokaci ya yi ta cc, "Allah ya nuna mana lokacin nan. " Ya ce, "Amin" Ta ce, "To ta so mu je dinning dan abinci ya dade da kammaluwa kai kawai yake jira." Ya mika mata hannunsa wai ta tashe shi ta ce, “Kaima kasan ba zan iya ba in ba so kake ai haihuwar guzuma ba ɗa kwance uwa kwance yadda kake ɗinnan kace in dɗaga ka, kai ma kasan ba zan iya ba." Ya tashi yana dariya ya ce, "Laifinwa bake kike dirkamin abincin da zan karuba na zata santi kike tun da banji kina complai din ina sakar miki nauyi ba, ya karashe maganar yana daga mata gira. Ta yi dariya tana faɗin Alhaji Kafa girma." 38 IZGILI WHY JAMILA MUHAMMED Ya ce, To bara in gama cin abinci sai ki yi bayanin girman da na yi." Suka yi dariya. **** Yau kimanin sati uku ke nan yana yin zuwa na musamman domin ya san shin ita din wacece so yake ya wani abu game da ita yana so ya san gidansu, amma shiru kake ji babu ita babu labarinta jiya akan idansa aka shiga makarantartasu kuma yana nan aka ta shi ya dinga baza ido ko zai ganta amma komai irin hijabinta bai gani ba, gaba daya kansa ya dau chaji to me yasa bata zuwa makarantar a yan kwanakin nan ya rasa wanda zai tanbaya labarinta to yau din ma haka ya gama zagayanshi daga farkon titi na koki har karshensa, amma duka baba dantela dva va shiga damuwa. IZGILI JAMILA MUHAMMED To ko dai alhaji umar zai samu ne akan maganar gaskiya yana san sanin wani abu daya danganceta dai-dai nan ya ji wayarsa tana ringin ya dauka Alhaji Umar ne ya dauka bayan sun gaisa ya ce, "Kamar kasan yanzu nake tunanin kiranka sai kuma ga shi ka ri gani alhaji Umar mai akwai ya yi dariya ya ce, "Daman
🏠