NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 5 of 22

ILI JAMILA MUHAMMED Ta gangara inda Jana take suka jera zuwa titi Anty Meena yayar Jana ce uwa daya uba daya ita cc a biyu a gidansu tana aure a Yalwa bata taɓa haihuwa ba. Jana suna tsaye abakin titin,suna jiran adai-daita sahu kasancewar duk wanda ya taho zaka same shi da mutane saboda yamma ta yi tun daga nesa ya hangota ya ganeta ita ce zuciyarshi ta gaya masa ya tsura musu ido yau ma dai irin shigar da ya ganta da ita ce sai dai wannan ba hijabin Islamiyar bane shi wannan kalarsa maron ne kalar flat din takalminta ne kuma sanye take da Nikaf dinta babu abinda kake gani sai kafarta kasancewar Hijabin dogo ne sosai. Idonsa ya kai ga wadda take kusa da ita ya kalleta yaga irin shigar da ta yi gaskiya ya yaba da nutsuwarta da hankalinta yana. kallo sai tsaida abin hawa 27 IZGILI JAMILA MUHAMMED suke amma ba su samu ba ya wuce ta gabansu yana ci gaba da fadin kamun kanta to shi dai duk ganin da yake yi mata cikin nutsuwa yake ganinta bai ma taɓa ganin fuskarta bato me yasa ya ji wannan samarin suna fada mata wani suna wai kanti ya juya baya mai hakan ke nufi? Wata zuciyar ta ce, masa kawai dan sunga ba kalarsu bace shi yasa suke jin haushinta har suke Igaya mata wani suna haka ya dinga tunani harya isa gida. ** . Hadiya tana sharar tsakar gida ta ji sallamar babbar kawarta tata Jana. Jana kawar Hadiya ce tun suna yara sun yi mutukar shakuwa ta yadda babu wadda za tai kwana biyu batare da ta nemi 'yar uwarta ba duk da babu ta yanda za ai su hadu batare da sun kafsa ba anan dai na yi musu da maganar Malam bahaushe da 28 IZGILI JAMILA MUHAMMED ya ce, sai hali yazo daya ake abota to waɗannan aminan junan su sam ba haka bane dan ko wace da inda ta dosa inda hakan halaiyace inda Jana ta kasance mai san gayu da kece raini tana da rawar kai mutuka ga saurin fushi amma bata da wuyar saukowa. Tana da kirki bata kuma da kyashi ko hassada ita in dai dan uwanta ya samu to ji take tamkar ita ta samu sannan bata da rufi duk abinda ya dameta kai tsaye zata gayawa babbar aminiyarta bban abinda yasa suke samun matsala da kawartata shine ita dai Jana Allah ya yo ta mai san saka kananun dinkuna ce kuma idan tasa ba zata sami mayafi mai yalwa ta rufe jikinta ba, sai dai irin na 'yammatan zamani ita tana jin bakin ciki ganin yadda kullum Hadiya take faman jibgawa jikinta dogayan hijab har da su 29 IZGILI JAMILA MUHAMMED nikaf, sai kace a zamanin jahiliya ga dai kyau dan asali kyau zalla amma bashi da amfani tunda kullum ana rufcwa masu so basu gani ba bare su yi sha'awa yayinda Hadiya tata kasance kasance. marasan magana sannan bata san raini ko wulakancin sam bata da saurin fushi amma kuma bata da wuyar saukowa tana da shagaɓa mutuka da sangarta in dai a gaban Abbunta ne da Innarta tana da tausayi ita abu kankani sai ya sata kuka shi yasa Jana take ce mata mai arhar hawaye, ita abu kaɗan sai ya sata kuka. Ta dago da sauri tana dariya Jana ta kalleta ta dauke kanta ta karasa gefen tabarman dake shinfide suna gaisawa da Inna Hadiya tana sharar tana dariya dan ta san lefinta ta san kuma shi yasa Jana ta zo tana karasa sharar ta wanke hannuwanta 30 IZGILI JAMILA MUHAMMED. ta karaso kusa da ita tana fadin "Kawata ya dai.?" Tana dauke kanta Hadiya ta guntse dariyar da ta cika mata ciki ta ce, "To ta so mu shiga ciki sai ingaya miki uzurina da abinda yasa ban aiko miki da wuri ba." Jana ta bita ɗakinsu ta zauna kan 'yar yalolowar katifar Hadiya wadda saboda sidewa ta dawo tamkar tabarma, ta kalleta ta ce, "Uhm Ina jinki faɗa min dalilin da yasa da kika san ba zaki je ba me yasa baki aiko min da wuri ba.?" Hadiya ta zauna kusa da ita ta ce, "Ai ya kawata ni ma ba haka na so ba na san Bilkisu Ibrahim ba zata ji dadi ba, babu daya daga cikin mu daya je." Jana ta harareta ta ce, "Waya ja? Idan bake ba da kika san ba za ki je waliman nan ba tunda wuri ba sai ki aikomin ba in sami abokin tafiya kawai 31 IZGILI JAMILA MUHAMMED sai dana shirya ina ta jiranki sannan zaki wani ce min Inna bata nan, shi yasa ni ma Faina ya ɓaci kawai nace to nima na fasa zuwa. " Hadiya ta ce, "Haba sister me yasa kika fasa ai Amiru ɗazu ya gayamin dana ce ya je ya gaya miki ki bani kayan walimar ya ce ke ma ba ki je ba. Jana tana faɗin ‘yar rainin hankali bayan sai da kika bari duk 'yan tafiyar sụn tafi sannan kika wani aikomin ai na ji haushinki sai kuma daga baya na ji daɗima da bamu je ba. Hadiya ta ce, "Saboda me? Yanda kika kwallafa ranki akan walimar nan. " Jana ta tura mata wata leda da ta ganta da ita ta ce, "Bisket da chacolate din nan, na Bintu ne da Aliyu shi kuma túraren naki ne. 32 IZGILI JAMILA MUHAMMED Sannan ta ɗauki post din ta ta ajiye "ta a kusa da ita ta bude ta fito da wata dalleliyar waya mai shegen kyau daga gani kuma zatai dan karan tsada sabida haduwarta, Nokia ce gaskiya ta hadu. Hadiya ta ce, "Gaskiya mutuniyata wannan wayar ta hadu karshe. Kuma daga wa?" Jana tana daga kwance sai
🏠