NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 4 of 22

na masu yi suyi." Hadiya ta ce, "Yanzu duk wannan baza eye shadow da wannan jam bakin da kika gabza ba ki yi minti sha biyar kina yi ba, ai ban miki magana ba, to sanin ki da nayi naga ko kin gama fentefenten naki ba gama kwalliyar bace dan sai ki kara 20 IZGILI JAMILA MUHAMMED PROSTY wani minti sha biyar din kawai kina kallon madubi kina kara baza powder ja na ta ajiye sosan da take shafa powder ta kara gyara zaman ɗaurin ɗankwalinta ta ce, "To da zaki ishe ni da Ina ta shafa powder ca nake ke ma kin shafa ko ke naki ba sai ni zaki hurawa wuta.' " baki gaAnty Meena ta shigo tana fadin ita ai shafawar masu hankali ta yi ba irin taki ba da sai a kusan karar da ita ashafawa daya, ke in dai zakiyi kwalliya sai ki shafa powder wajen sau goma. " Jana ta cuno baki tana kunkuni ita kuwa Hadiya dariya take mota ta ɗauki Hijabinta ta saka gami da ɗaura nikaf dinta ta ce, "To fi'ili madi ai sai mu tafi ko?' Jana ta kalleta wani takaicinta ya kamata tace dan Allah dubeta haka kawai kisa kanki a Uku ki dinga yawo cikin 21 IZGILI JAMILA MUHAMMED wannen zirmemen Hijah ki wani rufe fuska ke ba matar Liman ba zafi duk ya damc ki, dan Allah dubeki duba kayan dake jikin ki Hadiya tai saurin daga Nikaf dinta tana kallon Jana ta ce "Mc kayan nawa su ka yi.?" Jana ta ce, "Riga da siket ne ajikinki sun yi miki bala'in kyau sun yi cif-cif a jikinki tamkar ajikinki a ka dinka su saboda kyan da kayan su kai miki amma zaki kassara rayuwarki ki rufewa mutane, to ba a haka bane zaka samu mai son ka wanda zai ganka ya ga ka yi masa amma ke kullum zurum-zurum cikin hijab har da su nikaf shi yasa har yanzu baki da saurayi ko daya, to yaushe mutum zai ce yana sanki alhalin bai ga abinda yai masa a jikinki ba bare ya ce, yana son ki. Ta cije gefen danyatsanta ta ce, "Wayyo Allah garin dadina nesa in ji 22 IZGILI JAMILA MUHAMMED Angulu da ta lefa masai ai wallahi da ni Allah ya bawa farin ki gashinki, dirinki idanunki muryarki, wallahi ba karamin yaki zan yi ba don sai na saka samari runtsċ ido sai na daga musu ganye da duk wankan da nai sai na sumar da samari warwas Allah yai miki kira ba ta Allah Sarki ba ya yi miki halitta ba wadda miji zai ce shiga daka na yi ba, Amma kina cutar da masu sanki ni na tabbatar ko sau daya kika cire Hijab din nan da wannan Nikaf din na tabbatar sai kin saka maza karo." Anty Meena ta kaiwa bakin Jana duka ta ce, "To taki yin yadda kike so ke ganin fito da tsiraici waje shine wayewa to wallahi ba wayewa bace, sai ci baya wanne namijin ne kin gama tallar Nono da kugu awaje zai kwashe ki sai kace mara mafadi to bara in baki misali ke ce 23 IZGILI JAMILA MUHAMMED kika ga a titi ana sai da cincin ga wani abude kura da iska duk sun koɗashi ga kuma wani a cikin glass a rufe sai mai cincin zai baki nawajen nan wanda saboda kura da ta badeshi har ya fara canja kamannin shi, "Ai na san babu ta yanda za'ayi ki yarda ya baki wannanAlhalin kina ganin yarda yake sai dai ki ce na rufen nan kike so, saboda yafi mutunci to haka ma maza suke kallan duk wata mace mai bayyanar da jikinta mazan titi suna gani haka suke kallanta tamkar wannan buɗaddan cincin din da dattin duniya ya gama badeshi.. Hattara dai mata masu irin wannan hali masu gani cinyewarke nan to wallahi ci baya ne ba cinyewa bane bar ganin a nayi miki layi a gidan ku dan kina irin wannan shigar to ina mai tabbatar miki duk cikin masu zuwą gun naki babu 24 IZGILI JAMILA MUHAMMED wanda yake zuwa da zummar aure sai dai da niyar wata bukata ta shi, kuma da bukatarsa tabiya ba zai kara ko kallon inda kike ba to talla ki kai shi kuma ya taya kika sallama to kin ga kuwa taya zai kai ki gidansa harki zama uwar ‘ya'yansa, ke ma kin san (Impossible) Jana ta dauki ɗan yalolon mayafinta daya dace da atamfar jikinta da akaiwa dinkin riga da siket sun kamata dan-dam ta dauko post dinta ita ma kalar kayanta. Ta ce, "Sai mu tafi Sayyada." Anty Meena ta ce, “Ko baki faɗa ba mutane zasu fada su ce ita din Sayyada ce ke ko kunyar jerowa da ita baki ji ba, ita ta yi shigarta ta kirki mutum duk na cinsa ba zai ga ko ina nata ba, amma ke dubeki dan Allah wallahi Jana ki yiwa kanki faɗa, ki yi koyi da Hadiya ki dinga komai na ki da nutsuwa." 25 e. 2 IZGILI JAMILA MUHAMMED Jana ta figi ledar da Anty Meena ta shigo musu da ita, turaren wuta ne da Humra da take siyar da su ta basu turaren wutar ta kaiwa Iya mahaifiyarsu da kuma Inna mahaifiyar Hadiya Humrar ta suce ta basu sannan ta mikawa Hadiya dari biyu ta ce su hau adaidaita sahu. Hadiya ta ce, "Wallahi ki barshi Anty muna da kudin Mota." Anty Menna ta dan zare mata ido ta ce, "Karбi mana ai na san kuna da kudin motar na baku.” Hadiya kasancewarta mai da'a kuma ba a ai musu tarbiyar jayayya dana gaba, yasa ta karɓa tai mata godiya ta rakota har soro. A kokafar suka ga Jana ta cuge tana ta faman kumbure-kumbure. Anty Meena ta ce, "Ku gaishesu." Hadiya ta ce, "Za su ji." 26 IZG
🏠