i dai in
bude tsarabar nan in raba kowa ya dauka
13
IZGILI JAMILA MUHAMMED
dan naga dattijo na ya kagara kowa ya ci
ko ba haka ba."
Ya ce, "Hakanne Abbu su ka kuma
yin dariya."
"
Malam Usman ya kalli Hadiya ya
ce, "Zo ki dauka ki wanke.
Ta ce, "To"
Cikin nutsuwarta ta dauki ledar
daya tureta gefe ta dauko wata 'yar
madaidaiciyar roba ta juye abin dake ciki
mangwaro nene lafiyayyo lafiyayyo masu kyau
manya manya. Ta wanke su tas sannan ta
kawowa Innarsu dan ta san ita zata raba
dai dai nan Bintu tai sallama ta shigo
mallam ya kalleta ya juyo da kallonsa ga
Innar da take raban Mangwaron ya ce.
"Wai shin Lariya bansa dokar fitar
yaran nan waje ba, In dai fitar ta wuce
cikin wuce wannan lokacin.
14
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Cikin tsananin ladabin Innar har da
dan dukawarta daga kan kujera ‘yar
tsugunne da take kai ta ce, "Ka fada.?"
Ya ce, "To to raina ni a kafara yi da
zance bana san abu ayi sanin kanki ne
babu abinda natsana irin a dinga barin
yara mata suna kaiwa magriba a waje, har
nake kafa miki misali da cewar ko aike ne
in har magriba ta sawo jiki to ki dinga
hakura har na dawo ni sai in je, shi ma
dattijo sai da nai masa faɗa, da har na
same shi a waje yana wasa ke kuma babu
ruwanki da kisa ayi kiransa ya dawo gida
tun da yamma ta yi ko.?"
Inna Lariya cikin ladabi gami da
kwantar da harshe ta ce, “Ka yi hakuri
Malam dan Allah Allah ya huci zuciyarka
wallahi dole ce ta sa na aiketa kuma
bama ta da lafiya ba, gidan babansu na
aiketa dan dazu Iya Saude ta aiko min
15
IZGILI JAMILA MUHAMMED
idan nadaka garafuni in bata to nai duban
duniyar nan ban gan shiba sai bayan ɗan
aiken ya tafi sannan na ganshi dan sai da
na caje ɗakina sosai to shi ne da suka ta
so Islamiya na ce tai maza ta dawo amma
dan Allah ka yi hakuri insha Allahu haka
ba zata kuma faruwa ba, ya sauke ajiyar
zuciya ya ce,
"Allah yasa."
Ta yi saurin cewa "Amin"
Tai wa Abbu Sannu da zuwa sannan
ta mika ledar da Iya ta aikota ta kawowa
Innarta su Innar ta bude taga curin fura ne
da kuma nono mai kyau ta ɗaure ta kalli
Malam ta ce, "Yau shi kenan ba za a ci
irin tuwan nawa ba dan ga shi nan iya
tayi maka haji da Umra."
Malam Usman ya saki dariya ya ce,
"Lallai kuwa yau tuwanki ko kallo bai
ishe ni ba dan haka yi maza ki dama min
16
"
*
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kafin in dawo daga masallaci dan ga kira
nan a na yi."
Yana gama maganar ya karɓi butar
da Hadiya ta miko masa ya fara alwala su
ma gaba daya suka mike dan bada farali
Aliyu auta ne yai zaune yaki ta shi. Inna
ta ce, "Ya dai dattijo.?'
Ya ce, "Inna mangwaro."
Nan tai dariya ta ce, "Kayi sallar
mana tukunna ko kaga nace su dauka kai
kuma na hanaka.”
"
Ya mike da sauri damin yabi
Abbansu masallaci dan in dai bai je ba zai
iya cewa kada a bashi mangwaron tun da
bai bi jam'i ba.
****
Yau ma kamar ganin da yai mata
kwanakin baya sai dai yau tana rungume
da alkur'ani ta zo ta wuce ta gabansa
cikin nutsuwar nan tata ya rakata da idanu
17
IZGILI JAMILA MUHAMMED
tana dan yin yanga baya ya ji samarin da
suke kofar gidan da yake makoftaka da
gidan Alhaji Umar mai akwai daya
saurayin ya san shi dangi tane ɗaya ne bai
sani ba, ɗaya saurayin ya ce, "Gata nan fa
mutuniyar taka."
Kanti ya juya baya. Bashi ya saki
dariya ya ce, "Wallahi Allah ya suturu
bakui in ji kishiyar mai dorina ina zan
iya."
Kanti ya juya baya "Ai ba zan iya
koyaushe dan cinikin da nayi akasuwa su
kare akantin nan mutane ba.
Nura ya ce, "Yanzu ina jin ta daina
tunda yai mata illa."
29
Bashi ya ce, "Ta daina me? Kallo
kafarta ka gani mana malam tamkar ta
turawa saboda tsahar mankanti fuskarce
dai dai ta ga ji da man shi yasa ta lalace
take rufeta yarinya sai shegen jiji da kai
18
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ke da fuska ta riga tai dameji har kece me
wani ɗagawa mutane kai."
Su ka sake dariya suka tafa Alhaji
Mansir ya ce, "To me ye ma'anar Kanti.
Ya juya baya sun santa ne ko̟ ku ma
dai ita ma bata da nutsuwa tamkar su, dan
kallo daya za kai musu ka san su din
kwararrun 'yan duniya ne, haka zuciyar
Alhaji mansir ta dinga masa tambayoyi
barkatai wanda ba shi da amsar su, dai
dai nan Alhaji Umar mai Akwai ya fito
hannunsa dauke da wasu takardu ya
karaso inda Alhaji mansir yake tsaye
jikin motarsa, ya mika masa hannu gami
da cewa “Ga_su_nan ka duba su, jibi
jibin nan nake son tafiya Kaduna akan
aikin makarantun nan.
"
Ya ce, "Insha Allahu zan yi
kokarin ganin na gama su jibin su kai
sallama ya shiga motarsa ya tafi.
19
IZGILI JAMILA MUHAMMED
BAYAN SATI UKU
Hadiya ta duba agogon dake daure a
tsintsiyar hannunta ta kai dubanta ga Jana
data ke ta faman baza powder Hadiya ta
ce, "Dan Allah Jana kibar saka powder
nan haka kin ga yamma ta yi kada Abbu
ya dawo ya tarar bamu dawo ba gobe ba
zai sake barina fita ba."
Jana ta dan dauke idonta daga
kallon Mirrow ta ce, "Dan Allah kada ki
takuramin ki barni in yi kwalliyata cikin
nutsuwa dan na sanki da shegiyar
hayyata in ke bakya abu sai ki ha