NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 20 of 22

e a Alu Aɓenue sai kuma abokina kuma aminina shi kuma sunansa Alhaji Mansir kwangila haifaffin 124 IZGILI JAMILA MUHAMMED garin Gombe ne amma anan garin shi yake yana zauna ne a Sultan Road kuma shi ne wanda yai dalilin zuwannmu nan.” " Malam Usman ya ce, "TO madalla Allah dai yasa lafiya .?" Alhaji Yakubu ya kuma sakin dariya ya ce, "Lafiya kalau, alhaji Daman dai yaga 'ya wajenka ne ya yaba da hankalinta da nutsuwa gami da tarbiya irin ta gidan nan shi ne ya yiwa dansa kamu, in dai babu wanda akaiwa * alkawarito yaran gurinsa yana son ta. " Malam Usman ya ja shiru na lokaci mai tsaho sai can ya ce, "To Alhaji hakikanin gaskiya ban yi mata miji ba, kasancewar ban bata damar sauraran samari ba, saboda karatu, take duk da dai ta kusa gamawa dan saura wata uku ne kurum ya rage ta gama, to amma wani hanzari ba gudu ba, kamar na so na ji 125 IZGILI JAMILA MUHAMMED kace shi Alhajin ne yayaba da ita ba shi yaron bane, ya ganta, ya ga yana son ta ba. Alhaji Yakubu ya cc, “Haka nace to mu din mu na yi ne kamar yanda shari'ar ta tsara gurin neman aure kuma muna bin yadda addini ya tanadar cewar idan zaku aurar da 'yar ku, hakkin iyaye ne su nemawa ‘yarsu miji na gari haka ma mijin suna iya zaɓa masa mata ta gari shi yasa muka zo da karfinmu saboda tarbiya irin ta gidanka mu kai kwaɗayin hada zuri'a da kai." Malam Usman ya sauke ajiyar zuciya, Gaskiya ya gamsu da duk wani bayani da kuka yi kuma shi ma zai so hada zuri'a da su dan ya fahinci su din dattawan kwarai ne, kuma ya gane su din ba daya suke da sauran ,masu kudin wannan zamani ba, da karan gidansu yafi ye musu talaka sau dubu, basu talaka mutum ba, ba wai dan kuɗinsu ba sai dan kamala da mutuncin da suka nuna ko 126 IZGILI JAMILA MUHAMMED kusa ko alama bai ga wani wulakanci ko tsantsanin da suka nuna masa ba tun zuwansu lallai ku a cikin masu kudin su din daban suke ya cc, su dan ba shi lokaci zai tuntuɓi mahaifyar yarinya ko da wanda ita yarinya take so suka cc to babu damuwa kamar yaushe yake ganin zasu dawo dan su ji yadda ake ciki ya ce idan Allah ya yarda nan da kwan uku suna iya dawowa su kai masa godiya ya ce, Ai babu komai ya rako su har kofar gida gurin motarsu ya nayi musu fatan alkhairi da addu'ar sauka lafiya.- Suna karayin musabaha, Bintu ita da dan Auta Aliyu suka dawo daga Tahfiz, suka durkusa har kasa suna gaishe su, suka amsa cikin fara'a gami da jin dadin yadda aka karramasu. Alhaji Yakubu ya fito da kuɗi a aljihunsa har sun mike ya kira su, suka farasa gabansa sosai suka kuma durkosawa ya mifa musu sababbin ‘yan dubu dubun da 127 IZGILI JAMILA MUHAMMED ya kirgo guda goma ya mika musu yaran tamkar ashim film suka wani zabura a tare gami da mikewa har suna hada baki gurin cewar A'a mun gude su kai hanyar shiga gida Alhaji Yakubu ya juyo da kallansa ga Malam Usman ya ce, "Haba Alhaji ya za kai min haka yanzu ba zaka sa baki su karɓa ba, ni fa na niya ba wai rokona su ka yi ba, cewa nake ka karanta babu mai mai da hannun kyauta sai shadani, hakan yana da kyau hana yaro amsar Abubuwa a hannun mutane. Amma fa idan bai san su ba in dai mutum ya san yaro ka ba shi abu bai karɓa ba, sai ka ji babu dadi duk da yake karбar ma ko da yaron ya san yanda ya ba shi to hakan ma koyan kwadayi ne, cewa nake a iya zaman da mu ka dan yi yanzu da kai ka yarda damu din masoyanka ne, tunda har muna son hada zuri'a da kai nan ba da dadewa ba, insha Allahu, ai ina ganin mun zama daya ko ba haka banc.?" 128 IZGILI JAMILA MUHAMMED Malan Usman ya cc, "Hakkun amman ina ganin Alhaji kudin nan sun yi yawa." Alhaji Yakubu ya ce "Ba wani yawa da su ka yi in dai ka dauke mu da zuciya daya, kuma 'yan uwa ka ɗaukcmu." Malam Usuman ya cc, "Wallahi da zuciya daya na dauke ku. " Alhaji Yakubu ya ce, "To In dai haka ne to ka sa su su karɓa tun da ni ma babansu ne. 99 Malam Usman ya yi murmushi kawai ya juya zuwa soran gidan inda yai kiransu ya dawo gurin su Alhajin yana karayi musu godiya su kuma suka ce babu komai sune da godiya. Bintu ita da Aliyu suka durkusa suka ce, "Abbu gamu ya nuna su Alhaji ya ce, "Alhaji ne yake kiranku.' Suka karasa gurinsu ya mika musu kudin ya ce, "Abbunku ya ce, ku karɓa.' " 129 IZGILI JAMILA MUHAMMED Suka juyo suna kallon Abbun nasu. Malam Usnam ya ce, "Ku yi musu godiya." Ai fa yara suka dinga zararo godiya sai da Alhaji Mansir ya ce, "ya isa ku je gida ku sayi Buskit.' " Suka ta shi cikin nutsuwa suka shige gida babu wata harguwa irinta sauran yara, komai cikin nutsuwa suke yinsa nan dai suka sake sallama sannan suka ja motar suka tafi, da alkawarin za su dawo nan da kwana ukun. ****** Da daddare bayan sun gama cin tuwon dare sun baje suna shan iska suna kuma hira Malam Usman yai gyaran murya ya ce, "Lafiya baki tambaye ni in da dan autanki ya samu kudi ba.?" Inna ta yi dariya ta ce, "Malam ke nan ai tunda Hadiya ta bani kudin ta ce su Binta ne suka cc ka yi baki shi ne bakin suka basu 13
🏠