NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 2 of 22

gurin can, basa kansa. Ya lura ya kurawa guri daya ido ya kalli inda yaga yana kalla bai ga komai ba sai kawai mutane da ya ga suna zirga zirgarsu yawancinsu duk 'yan Islamiya ne da suke ta tururuwarwar tafiya zuwa gidajen iyayen su. Ya dan taɓa kafaɗarsa gami da kiran sunansa. Alhaji Mansir dan kimanin shekaru saba'in da biyar, ya yi firgigit ya juyo gare shi tamkar wanda ya ta shi daga barci ya ce, “Am! Alhaji Umar me kake cewa ne?" 7 IZGILI JAMILA MUHAMMED Alhaji Umar ya ce, "Ina hankalinka ya tafi ne?" Alhaji Mansir ya ce, "Na dan tafi wani tunani." Alhaji Umar ya ci gaba da yi masa baya ni ya ce, “Mun yi dai dashi Nan da sati hudu zai turo mana da cikwan kudin dan wallahi sai da nai masa jan idanu, in shi yana takamar dan zamani ne to ni nashekaran jiya ne, dan na ga jiya naga yau, kuma sai dana jaddda masa in har lokacin yayi na ji babu labari to wallahi kotu zan maka shege dan baka ga yadda ya dinga bani hakuri ba da ya ga na je masa ba sauki yana ta makyarkyata da ya ji zancan Kotu yana bada hakuri nan na taho na barshi. ". Alhaji Mansir ya ce, "To shi ke nan ni zan tafi yadda mu kai da Alha ji Auwal game da aikin titunan nan zan ma waya.' " IZGILI JAMILA MUHAMMED Alhaji Umar mai Akwai ya ce, "To babu damuwa," Su kai Musabaha. Alha ji Mansir ya shiga dankararriyar motarsa ya tafi. Zaune take atsakar gidansu tana tankaɗan dawar tuwan dare Innarsu Kuwa tana daga can gefe tana kaɗa miyar Kuka, kuma suna ɗan taɓa hira mahaifinsu ne Malam Usuman ya yi Sallama gaba ɗaya suka amsa masa ya shigo hannunsa rike da dan autan Innarsu ɗaya Hannun kuwa bakar leda ce yake rike da ita Inna Lariya ta saki Kadin miyar da take yi ta shimfida masa wata sabuwar tabarma da take jingine gefe guda tana masa sannu da zuwa Hadiya da sauri ta karɓi ledar da take hannunsa ita ma ta nai masa sannu da zuwan Inna ta dauko kofin silbar dake ajiye a gefe guda 9 IZGILI JAMILA MUHAMMED wanda aka ci ka shi da sassanyar ruwan Tulunta ta a jiyewa maigidan tana karai masa sannu. Ya sha ruwan sosai sanyinsa ya ratsashi sannan yayi hamdala ya dire kofin shima ya nai mata sannu da gida. Aliyu dan Autan Inna yana daga gefe sai murmushi yake faman dukawa gaba daya ji yake tamkar an sakashi a gidan Aljanna saboda dadi ya san tunda yaga Abbansu da leda yasan yau da cin kayan dadi, shi yasa ji yake tamkar zai sume saboda murna, shi ma zai nunawa su Abdul Abokinsa kayan dadin da Abbansa ya siyo musu ko sa dainai masa gorin babbansa baya siyo musu tsarabar kasuwa kullum, Abdul sai ya yi masa dariya saboda shi Abdul din babansu ko da yaushe ya dawo daga kasuwa sai ya siyo musu kayan dadi su lemo, ayaba, . 10 IZGILI . JAMILA MUHAMMED abarba, Kwai, dafaffe, Biskit, youghort, wata rana har da gasheshen nama ko Kaza kuma ko babansu bai dawo da wuri ba to da sassafe sai Abdul ya ajiye ya nuna masa dan haka shi ma yau tunda Abbansu ya siyo musu tsarabar kasuwa to shi ma ba zai ci ba sai ya ajiye da safe ya nunawa Abdul ya dai nai masa dariya yana cewa babansu baya yo musu tsaraba idan zai dawo daga kasuwa, kalubalenku iyayan yara gaskiya da yawa iyayen yara abinda muke bama kyautawa yadda zamu dinga bawa yaranmu abu suna fita da shi suna nunawa yaran makota ko kuma yaran abokan zaman mu idan gidan haya ne ta yadda zaki ga an bawa yaro abu ya fita da shi cikin yaran gidansu yana ci a irin haka ana samun matsala babba, saboda wani yaran zai ‘yan musu wani kuwa sai dai ya ɗagawa sauran 11 IZGILI JAMILA MUHAMMED yaran hankali suna gani yana ci ba zai ba su ba, haka za ki ga yara suna rusa kuka duk su dagawa iyayen su mata hankali dole sai an basu irin abinda wane yake ci kun san yaro da gasa wata uwarma zaka ga ita ke tura yaranta waje cikin yara ya ci abin sai ka ga ta dauki abu ta ba shi sai ta maza je ka gurinsu wane ku yi wasa ko kuma fita tsakar gida gurin su wane ka ci mana, to gaskiya irin haka babu dadi ke dan asan kuna cin abu sai kin tura yaro dan a gani alhalin yana dagawa yaran mutane hankali. Akwai matan da suke cewa yaransu kada ka cinye duka mana ka rage da safe ka nu̟nawą su wane, da dai ire-iren haka, gaskiya mata mu daina irin wannan idan ke kuna da halin cin abu bai ka mata ki dinga turo yaranki suna dagawa wanda 12 i IZGILI JAMILA MUHAMMED kika san basu da halin wannan abin dan Allah mata mu daina Allah ka iya mana. Inna Lariya ta juyo tana kallon Malam din fuskarta fal da farin ciki ta ce, "Malam yau dai da alamar dawa Tai nama.? Tun da na ganka da leda.' " Shi ma murmushin ne akan fuskarsa ya ce, "Yau kam Alhamdulillah babu abinda zamu ce sai godiya." Ta ce, "Gaskiya kuwa, ba ka ga auta ba ma baki yaki rufuwa yarasa inda zai sa ransa saboda murna sai wata dariya yake ɓangalawa gaba daya su kai dariya har da Hadiya wadda take kaɗe zaninta ta matsar da garin tana cewa. "Abbu Kalli irin zaman ma da yai ." har da tankwashe kaafu.' Suka kuma yin dariya. Malam Usman ya ce, “Bar
🏠