NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 19 of 22

a dawo da sati biyu suka 'koma saban gidan da Alhaji Mansir din ya tamfatsa a sultan road a ciki ma a kai bude saban kasaitacciyar walimar kamfanin na Abuja da kuma murna dawowar ɗan lelan Alhaji wanda Alhajin ya sangarta shi ya taɓarashi, su ka kuma barshi yake yadda ya ga dama ba kuma tare da sun tsawatar masa ba. AN DAWO LABARI Hadiya ce sun kuye bakin murhu tana faman hura wuta taki ta kama kasan cewar icen ɗanye ne saboda yana yi na damina ta ɗago da idanuwanta da suka yi jajir saboda a tsabar hayaki tana amsawa 118 IZGILI JAMILA MUHAMMED yaron da ya shigo sallamar da ya yi, yaron ya ce, “Wai wani Awaje ya ce, na sallama da Malam Usman.?' Ta ce "Kace yana zuwa. Ta mike daga durkson da ta yi tana karkade jikin ta ta yi sallama kofar ɗakin. Innar ta su, in da baban nasu yake kishingide yana sauraren gidan radio kano suna gabatar da zaɓan yamma Inna kuma bata nan ta tafi dubiya, amma ta san tana hanya tunda yamma ta yi, duk da dai bata wani jima da tafiya ba, dan sai bayan sallar la'asar sannan ta tafi. Malam Usman yasa hannu ya rage radio yana amsa mata sallamar ta durkusata ce, "Abbu ana sallama da kai'a waje." Ya ce, "Wa ye.?" Ta ce, "Ni ma ban sani ba." Ya dauki hularsa dake ajiye a gefensa yana kokarin sawa ya ce, "To 119 IZGILI JAMILA MUHAMMED 'yar gidan Abbunta maza je ki ci gaba da aikinki." wata Ta saki wata dariya mai ban sha'awa ta tafi ta ci gaba da aiyukanta shi ma Abbun fitowa ya yi dan ya ga mai sallamar yana fitowa yaga tsadaddiyar mota ta dallare masa idanu, saboda kyau sabunta tai shurum a kofar gidan nasa, tana hutawarta daga gefe kuma wasu kasaitattun Alhazawan birni ne tsaye a jikinsu sanye da dakakkun danyin shaddodi, sai zabga daddadan kamshin turare suke irin nasu na manya, ya dan ja turjiya ya tsaya turus, yana tunanin ina mai sallamar yake dan shi ko kusa bai yi tunanin wadannan hamshakan mutanan sune masu sallamar ba dan ya san shi dai shehu Usman mai faci duk cikin mutanan daya sani yake kuma har 120 IZGILL JAMILA MUHAMMED kar dasu ba shi da irin wadannan balle har yai tunanin su ne suke sallamar... Sallamar ya ji an yi masa yai saurin dawowa daga tunanin da yake yi, ya amsa sallamar shi ma cikin sakin fuskar tamkar dai suma da suke ta sakar masa, murmushin. Shi dai shiru ya yi yana kallonsu daya ne ya farayin magana ya ce, "Mu ne muke sallama." Ya ce, “To madalla Alhaji Yakubu babban na hannu daman Alhaji Mansir dinne dai har yanzu yake maganar ya cc, "Daman Mun zo gurin ka ne da wata muhimmiyar magana wadda take bukatar zama dan ni din ba gwanin tsaiwa banc. Ya fadi hakan yana dariya, wadda ta bayyanar da hakorin farin gwal din da yake bakinsa. Malam Usman ya kalli rugujajjen kofar gidan nasa mai dauke da jarkasa 121 IZGILI JAMILA MUHAMMED tumumu irin jajur din nan ya kai dubansa gurgurarriyar kofar shiga gidan ta katako mai barazanar rusowa. Ya dan saci kallonsu dubi irin danyun shaddojin dake jikinsu yanzu haka zasu dansu a cikin jarkasar nan wata zuciyar ta ce, to ya za'a ayi ai sun kallo yadda gurin yake kuma a hakan suke san su zauna. Ya dubi Alhaji Yakubu ya ce, "To bara in kawo abin zama. " Suka ce babu damuwa ya juya da sauri çikin gidan ya same ni ina kwasar tuwon dare ya ce. "Hadiya maza shiga daki ki dauko sabuwar tabarmar ledar nan cikin girmamawa ta ce, "To" Ta dauko da sauri ya ce, "Yauwa ki zubo ruwan sha ki kawowa baki." Ta amsa cikin girmamawa ta saurin karasa kwashe tuwan ta dauko saɓanin 122 IZGILI JAMILA MUHAMMED kwanon sha sabo fil ta sake ɗauraye shi ta tuttulo ruwan tulun Innar mai dan karen sanyi ga shi ruwan dadi. Farin fenti jikin kwanon shan sun tai maka gurin fito da farin ruwan gami da tsaftar sa tamkar irin ruwan da suka saba amfani da shi, ta shiga ɗaki ta ɗauko zumbulelen Hijab dinta da nikaf ta saka ta ɗauki ruwan ta yi soro inda take jiyo maganarsu duk da dai ba sosai ake jiyo maganar ba ta yi sallama cikin siririyar murya ta durukusa har kasa ta gaishe su Alhaji Mansir da yake cike da fara'a gami da wani matsanancin farin ciki ganinta a zuciyarsa fadi yake tarbiya da dadi gami da biyayya da sanin girman na gaba sai gurin diyan talakawa dubi dai irin yadda zube gwiwa bibbiyu saɓanin 'ya'yan masu dà shi, wadda wata ma ko kallan arziki abokanan babban nata basu isheta. 123 IZGILI JAMILA MUHAMMED Masu tarbiyar cikinsu ne zasu gaishe su daga tsaye, ko kuma a ce, sannunku. Daddadar muryarta mai cike da nutsuwa ce ta katse masa zancen zucin da yake yi, ta ce, “Ga ruwa." Alhaji Yakubu ya suri kwanan da ta ajiye sanyin ruwan da ya ratsa kwannan ya ratsa tafin hannunsa yayi saurin bude murfin, ruwan garai-garai gwanin kyau ya sha sanyin ruwan ya kwaranya a tumbinsa yai hamdala Alhaji Mansir ma ya sha su kai godiya ga Allah. Alhaji Yakubu ya gyara murya ya fara da gabatar da kansa ya ce "Ni suna na Alhaji Yakubu Galadanci, ni haifaffen garin nanne a galadanci iyayena suke amman ni ina zauna n
🏠