tanadi gadon a Asibiti, saboda yasan sai
ya kwanta ciwo dan shi a ganinsa babu
babban abin kazanta irin abincinsu, dan
shi ko gani ya yi suna wani jagulan girkin
to fa ranar yini zai yi zuciyarsa na ta shi,
sai ya yi amai, zai ji dadi.
Shi a rayuwarshi babu abincin da
zai ci ciki lafiya baka lafiya irin abincin
mu na Nigeria.
Aiko dole Anty Nadiya take yin
irinsu tun bata saba ba har ta koya dan shi
da kansa yake yi, tana ganin har ita ma ta
iya take yi musu ai fa sai ta ga gaskiyar
Hisham abincin Nigeria yafi na kowacce
kasa dadi, a ido, zaka ganshi da tsafta
hade da ban sha'awa, baki ga shi da dan
karan dadi ranar da Hisham yai musu dan
haka hohoho! Zo ka ga wawa su gurin Al
Mubrak mijin Nadiya shi ma Balarabe ne
112
IZGILI JAMILA MUHAMMED
aiki ne ya kawoshi Germany amma
haifaffen Misra ne, danwaken fulawa ya
yi musu, da man gyada ziryan da yajin da
yasha magi ya yanyanka dafaffen kwai a
ciki ai ji su tamkar kunnansu zai tsinke
saboda dadi duk wata Momi take aiko
musu da ka yayyakin amfani irin na
Nageria har fulawa take aiko musu da ita
su kuka, daddawa, karkashi, kuɓewa
bushashshiya, zogale, wake, gyaɗa, man
gyada, dakakken yaji, manja, kayan
kamshi, man shanu, bushahhen kifi,
ogun, ayodi, da dai sauran kayayyakin
girki irin na Nigeria.
Aikuwa Hisham ya zage ya danɗasa
musu girkin da wata macen ma ba za ta yi
test ɗn na shi ba, komai cikin tsafta
Tentable gare shi kullum ga kalar girkin`
da zai yi ya iya wainar fulawa, wadda
baya gajiya da cinta, wake da shinkafa,
IZGILI JAMILA MUHAMMED
jallof din shinkafa ko taliya alkubus ma
ya iya, arayuwa tuwo ne kawai bai iya ba, shi ma ba wai towanne bai san yanda ake
ba ya san yanda ake yi tuka tukenne bai iya ba, duk sanda zai musu tuwo sai dai
ya nunawa Nadiya ta tuka. To bata iya ba
har ya koya musu, ita da Mijinta.
Wai shi ma yana san ya iya saboda
watarana ko idan Nadiyan bata da lafiya aikuwa tunda kowa ya iya shi ke nan idan
daga Hisham ne ya riga dawowa
makaranta sai ya girka musu abinci, idan Nadiya ce, sai ta yi dan ita ma karatu take anan jami'a da Hisham din yake, amma ba departement dinsu da ya ba, idan kuma mijin tane ya riga ta dawowa to shi
zai musu abincin.
Haka yai rayuwarsa cikin jin dadi gidan Anty shi tamkar kaninsu haka suka dauke shi ba dan ba shi yasa yake yadda
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ya ke so, a kuma lokacin da yake so
mahaifinsa ya shiga tashin hankali ne tun
randa ya kama kwalaben giya burjik a
dakinsa lokacin da ya dawo tun daga
sannan yake san ya yi aure ko ya rage
wani abun dan aure ni'ima gare shi yana
sa arage duk wani iya shegen da ake yi
tun daga lokacin yake tuntuɓarsa da
zancen amma shi Hisham din ya share
maganar a ganin sa me zai sa ya yi wani
aure idan banda takurawa kai da saka wa
kai tention to shi gara ya yi rayuwarsa a haka duk da ya san hakan da yake yi ba
dai-dai bane, ga tarin zunubin da yake ta
jibgawa kansa Zina ai babban laifi ne ko
da yaushe idan wannan tunanin ya faɗo
masa sai ya shiga ta shin hankalin irin
laifukan da yake aikatawa, ya yi ta tuba
gurin Allah amma ya kasa hana zuciyarsa
aikatawa, saboda shi din baya iya
'
IZGILI JAMILA MUHAMMED
daurewa ko ya ce ya daina da zarar wata
daga cikin 'yan matan nasa ta zo to fa shi
ke nan zai koma ruwa, saboda tsabar
sansa da 'yan mata suke yi ba shi yake
kiransu ba su suke zuwa har inda yake
kuma sai ya ga mai musu wulakanci
saboda shi din IZGILANCI halinshi ne,
ko dan jinin sarauta yana yawo a jininsa
ne, yasa yake da shariya, da tsare gida,
duk yanda kuke da shi karya ne ka ga
dariyarsa shi sam baya dariya sai dai
murmushi, shi ma mai gani daga Momy
dinsa sai Daddy dinsa sai fa idan ya yaba
da ke. Farkon haduwarku ba zai ce kin
masa ba, ko yai miki magana sai dai ya
dan yi miki murmushi, to har ku rabu da
shi ma, ba zaki kara ganin ya yi miki ba,
shi kuma duk yanda kika kai da nacinki
yawan lokacin da za ku yi ke da shi wata
ɗaya ne, da ga nan kuma sai wata, saboda
424116
IZGILI JAMILA MUHAMMED
yan matan su suke nuna masa kaunarsa su
suke kamar su ne namijin shi kuma shi ne
macen shi yasa yake ja musu aji yake yi
musu yadda yaga dama saboda su suke
binsa ba shi yake binsu ba.
Tir da wannan zamanin da 'yan
mata suke ganin cinye wace waye wace
dan kin buɗa baki kin cewa saurayi kina
san shi wannan ba ɗabi'ar kamun kai
bane, wai mai yasa mata muke wulakanta
darajar mu, muke banzartar da kimar mu
mace fa daraja gareta shi yasa Hisham bai
ɗauki mace wata tsiya ba, saboda ya cam
fasu duk matan waka suke basu da kintsi,
saboda bai taɓa haduwa da ta garin ta
kirki ba, wadda duk kyansa duk kuɗinsa
haka duk ajinsa kuma duk mukaminsa
karya yake ta bishi sai dai shi ya bita ko
da kuwa shi ne shugaban kasa, dan har
yau har gobe akwai na gari na kirki a
IZGILL JAMILA MUHAMMED
cikin 'yan matan masu kuma kima da
daraja, sannan kuma da yawa a duniya shi
din ne bai taba dacan haduwa da ta kirkin
ba yanzu watansa tara ke nan da dawowa
Nigeria.
Sanda y