octor
aikuwa sai da ya zama Hisham tun yana
Secondry dinsa ya fara Harka da 'yan
mata kasancewar kyakkyawa gaskiya
Allah yai masa halitta gaskiya Hisham ya
gama haduwa Hundred percent to jinin
.105
IZGILI JAMILA MUHAMMED
larabawa fa, da kuma fulani ga kulawa
dole a ga kyau dan usuli duk inda kake
neman kyakyakyawa to kana samun
Hisam sai a shafa fatiha, saboda kyau ne
tsabarsa babu mide babu abinda yake
kara masa kyau irin wadannan kyawawan
idanuwansa masu firgita 'yan mata ko da
yaushe zaka gan su a lumshe.
Hisham dogone amma ba irin
zankalkal din nan ba ne yana da dan jiki
watan murjewajiki dan shi ba irin
ramammun nan bane sanna kuma shi ba
mai jiki ainun ba ne, fari ne tas irin farin
larabawa kana ganin sa zaka san shi din
balarabe ne ta yadda ga shin kansa yake
akananɗe mai kuma azabar santsi da
baki irin na larabawa.
Yana da dogon hanci, bakinsa dan
dai-dai mai fararan hakora tas, tamkar
kankara, idanunsa a lumshe tamkar mai
106
IZGILI JAMILA MUHAMMED
jin barci yana kassara dubun nan 'yan
mata da wannan kallon na shi mai ratsa
JINI DA JIJIYA.
Hisham Mansir Kwangila ke nan
miskili mai murdadɗan hali yana da
tsare gira ba shi da fara'a tunda yake shi
bai san so ba, bai taɓa yin shi ba kuma
baya son yasan shi bare ya yi shi, duk
'yan matan dayake yi bai taɓa cewa yana
san su ba sai dan shi suce suna son sa...
Ya yi 'yan mata 'ya'yan manya wadanda ba zai iya kirga su ba shi din
mane min mata ne na sosai amma ba ko
wacce kuci ku bamu ba shi din sai kin kai
kin doke kin haɗu koma ki na da abinda
ya yi masa shi ne zai ce miki bukatarsa
shi yasa matansu suke rububinsa suke
kuma son sa.
Hisham sai da yai shekara goma sha tara a duniya sannan ya samu kanwa mai
107
IZGILI JAMILA MUHAMMED
a sarar
sunan Hajjo kakarsu wato Rahina, ake
kiranta da Ummita, Hisham ko da ya
kammala karatunsa bai dawo Nigeria ba,
wani kamfanin zane zane ne suka dauke
shi aiki sai da Alhaji Mansir ya yi da
gaske sannan ya dawo gida amma duk da
aka yadawo da ɗabi'ar nasara
duniya ya koyi yadda ake daga kwalba mata kuma yanda suke sonsa duk inda ya
shiga in dai da mata sai sun so shi dan
Allah yai masa farin jini in dai ya shiga
guri sai an so shi to kuma daman an ta shi
garin ida suka dauki zina tamkar ado,
kuma akai dacen shi din mai farin jinin
matanne da kansu suke yi masa tallan
kansu, burinsu dai da fatansu ya yarda dasu batare da ko kwandalarshi ba, su
abin alfaharinsu ne kamarsa hadaɗden
saurayi ya kwasa sai dai alhaji Mansir yai masa jan ido kuma an kammala ginin
108
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kamfaninsa na Abuja shi yasa ya matsu ya dawo domin ya kula da shi shi kuma
alhaji Mansir din ya kula da na nan Kano
din, ya kuma gaya masa ya siya masa fili
a nan cikin garin Abujan idan yana da
zanen gidan da yake sha'awa to ya turo
masa ta computer sai Ai masa kafin ya
dawo aikuwa har an kammala masa
hohoho dan da shi gaskiya gida ya tsaru tamkar wani shugaban kasa.
Gidan ya gama haduwa bada
dadewa ba ya diro Nigera kasarmu ta
gado, ya yinda ya kwashe tsayin shekaru
ba ya kasar dan tunda ya gama primary ya tafi sau biyu kawai ya zo shi yasa yaga
kasar ta canja masa, tamkar ba dan kasar
ba, dan duk komai ya canza masa, ‘yan
uwa ansha murnar dawowarsa, Ummita
kanwarsa ma sai murnar dawowar
yayanta take.
109.
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Bayan ya huta yai raban tsaraba
kowa aka bashi sai da yai wata biyu yana
hutawa sannan ya tattara ya koma Abuja
daman dawowarsa da sati akai
kasaitacciyar walimar dawowarsa, tare da
murnar bude kamfanin.
An sha shagali an kar kudi tunda ya
tare Abujan ya dada ci gaba da harka da
matansa giya tamkar ruwan roba ya
maida ta. Dan idan kuka ganta jejjere
cikin firji dinsa ka dauka lemo ne.
Gwani ne a harka da mata da kuma
wiwi, sai taba da ita ma ya kware gurin
shanta, to daga su baya karawa da komai
duk wani rashin tarbiya da ya koyo ya
kuma zubar da wanda iyayansa su kai
masa; to bai daina sallah ba, kuma yana.
yinta a kan lokaci, duk yanda ya kai da
sheke a yarsa to da zarar lokacin sallah ya
yi to zai watsar da koma mai yake, sai ya
110
IZGILI JAMILA MUHAMMED
sauke farali, Hisham yana da mutukar
tsafta ga
ya
shi kuma da tsantsani na jaraba.
Ba ko wanne abinci yake ci ba, sai
kina da maşifar tsafta shi a duk gidansu
idan ba Momi ce tai masa abinci ba ba
iya ci, da ba yacin girkin 'yan aikin
gidansu, dan haka ba kowane restaurant
yake cin abincinsu ba, sai irin kasaitattun
nan, wanda sai manyan garin na Abuja,
suke zuwa to irin su yake iya cin nasu,
koma sai ya bada tsaftar gurin da
ma'aikatansu zaka sha mamaki, mutuka
yadda ya dauki al'adun turawa, da
ɗabi'unsu to sai kuma bai dauki cimarsu
ba gaba daya ma ba zai iya cin irin
abincinsu ba, dan tunda yake bai taɓa
ɗanɗana irin abincin nasu ba, kuma ya
ɗauki tsawan shekaru goma sha tara
zuwa a shirin a turai amma bai taɓa gigin
dandanar cimarsu ba, don in har ya ce,
IZGILI JAMILA MUHAMMED
zai dandana to fa babu shakka sai ya