NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 16 of 22

ro mahaifin Zalifa watan Wazirin Sarki Misra ya dira duk mai bukatar zuwa Nigeria. To fa ga jirgi nan a kai ka a dawo da kai, haka akai taron suna lafiya a ka gama lafiya Jariri ya ci suna Hisham. Hisham ya ta shi yaro mai-nutsuwa gami da hankali amma fa miskili ne na gasken gaske shekararsa biyu a duniya Allah ya yiwa kakansa Alhaji Bawa rasuwa, rasuwar da ta girgiza duk wani mutum daya kwana ya ta shi a cikin garin na Gombe jama'a sun ji mutuwar mutum na mutane irin Alhaji Bawa, mai kirki 99 IZGILI JAMILA MUHAMMED mai taimakon bayin Allah mai hidima a gurin jadda kalmar Allah. Ayyukan da yake gami da taimakon da yake sai dai Allah ya biya shi Islamiyyoyi da masallatai fanfuna burtsatse babu wanda yasan adadin da ya yi a cikin birnin na Gombe da ma kauyikansu sai dai mu ce, Allah ya ji kansa, halinsa na gari ya bishi, mutuwar Alhaji Bawa da shekara Alhaji Mansir ya tattaro ya dawo Kanon dabo mai mata mai mota mai dala da gworon dutse. saboda harkokinsa sun fi yawa a can kano da Abuja, a inda ya kera gidansa a Zoo road suka tare sai dai duk karshen wata yake zuwa Gombe domin duba hajiyar, sai da ya kaɗa ya raya ya ce, Hajya ta dawo amma ta tubure ta ce, babu inda zata saboda mutanan alhaji marigayi saboda duk wani abu da ake yi da babu 100 IZGILI JAMILA MUHAMMED wanda aka daina 'yan'yan ta maza sun tsaya mata musamman Alhaji mansir dan shi ne ya dauko kyauta irin ta mahaifinsa, da son talakawa mararshi, dan gaskiya yafi kannensa najib da Isma’il taimako dan su da Hajjo tai musu zancen duk wata ga abinda zasu kawo cewa su kai kai a bari wanda Baffa ya yi ya yi, ya isa, Allah ya bada lada. Batai mamakin jin irin wannan maganar daga bakinsu ba dan ta sansu ta san halinsu suna kyamatar talaka sun ce su da talaka ko a hanya, shi yasa kwandalarsu ba zasu bayar ba, dama da mahaifinsu yake yi ba asan ransu bane, dan dai ba yanda zasu yi ne, kuma saboda ba kudinsu bane, ko da yake shi najib sai da ya taɓa gayawa Hajjo gaskiya ta gayawa Baffa ya daina kashe musu kudi haka. 101 IZGILI JAMILA MUHAMMED Ta kalle shi da alamar tambaya ta ce, "Wana irin kudinku yake kashewa aikuwa babu kun ya babu tsoon Allah ya ce, Dukiyar Baffan nasu ai ta suce saboda haka gaskiya Baffa ya daina raban kudi da abinci ai sangarta su ake yi, su dinga zaman banza, zuciyarsu ta ida mutuwa, tunda suna da mai basu abinci har ma da nace fane, dan kada ta Allah ta kasance gadonsu ya zaru babu auki." Hajjo sai ta saka salati tana salallami fadi take oh ni Rahine yau naga. abinda ya ishe ni najib Allah ya shiryeka to ni dai ba za aji wannan maganar a bakina ba, idan ka matsu kai ka same shi sai kai masa maganar, shi yasa koda suka ce su ficikarsu bazasu bayar ba bata damu ba, ta gayawa Alhaji mansir ya ce, Dama bata yi musu magana ba. 102 IZGILI JAMILA MUHAMMED Hajjo kin san dai kome ye kike bukata zan yi miki su yarane daman niya dace in yi ko meye Hajjo ta ce, "Duk da haka kai ma ai zaka so su taimaka maka tunda abinda ai da yawa, kuma kamar yanda kudi suke zuwar maka suma haka kawai dai su haka Allah ya yosu in dai batu ne nasu bayar to fa ba za a ji bakinsu ba, saboda Allah rayuwa kuwa zata yiwu. a haka kana da shi ba zaka taimaki dan uwanka marasa shi ba. Alhaji Mansir ya ce, "Hajjo ki daina ganin laifinsu suna fa da iyali ga yara da wanne za su ji." Hajjo ta ce, "Da yake kai baka da iyalin ko haka dai ya dinga bata hakuri ya ce, tunda ya ce, zai iya zai iya dinne tunda mahaifinsu ya rasu, shi ya dauki nauyin yin sadakar da aka sabayi, duk safiya ana dama koko da kosan sadaka 103 IZGILI JAMILA MUHAMMED kuma kokon da sukarinsa bajau, da rana kuma ana yin wake da shinkafa da mai mutum sai dai ya nemi ya ji, kuma ba sai almajirai ba ko waye in dai yake ko ya kai kwanansa, duk girmansa sai an take masa shi abinci, duk ranar juma;a ana can ja kalar girkin da safe ana yin kunun tsamiya da fanke, da rana kuma ana yin tuwon shinkafa da miyar taushe, kuma gaba daya Alhaji mansir ne yake komai hatta da 'yan aikin da suke wannan aiyukan shi yake biyansu, kwandala babu ta wani dan uwansa kuma duk karshen Iwata yake zuwa ya saurari talakawan da mahaifinsa yake taimaka musu, wasu bikin 'ya zai yi babu gaba ba baya. Wani matarsa ce ta haihu babu Ragon suna wau rusaune ya rutsa da su, da dai sauransu duk kuma wanda ya kawowa Alhaji Mansir matsalarsa to sha 104 IZGILI JAMILA MUHAMMED Allahu sai ya taimaka masa sai mutumin nan ya yi farin ciki ya saka masa albarka. Hisham ya yi Primary dinsa wata tsadaddiyar makaranta dake cikin birnin na Kano mai suna Attaufeek Iliman an tahafees yaro ranar da ya gama primary, to ranar aka masa bikin sauka to shi ma Hisham haka daga nan sai alhaji Mansir ya kai shi Germany gidan kanwar Hajiya Zalifan watan Nadiya da take aure a can suke zaune a can ita da mijinta sai dai basu haihu ba a can yai Secondry dinsa yai kuma jami'a. Hisham ya zaɓi ya gaji dadinsu watan dai yana san zama contr
🏠