AMILA MUHAMMED
da muke bukata buka, sannan yana da
kamfanin Tumaturin gwangwani sannan
yana da wani kamfani amma hadin
gwiwa ne, a jafan da suke kera takalma
masu shegen kyau, matar Alhaji Bawa,
daya mai suna Rahina, ana kiranta da
Hajjo Allah ya albarkace su da ‘ya'ya
bakwai uku maza hudu.
Mata ta farko mace ce mai suna
Binta da ake kiranta Batulu, sai na biyu
mai suna Mansir, daga mansir sai Barira
sannan Hindu, sai najib, sai Safiya, da
kuma dan autansu, Isma'il gaba dayansu,
sun ta so cikin kulawa hade da tarbiya
irinta addinin musulunci sam Alhaji
Bawa shi da Hajjo basu saki yaran sun
sangartasu ba, wai dan kasancewar
mahaifinsu, wani ne, sun basu tarbiya ta
gari dan gaba ɗayansu, sai da kowa ya
sauke sun yi karatunsu na boko amma
93
IZGILI JAMILA MUHAMMED
matan iyakar su secondry ake yi musu
aure Inna Batulu anan Gombe take aure
bata taɓa haihuwa ba.
.
Safiya Bauci take da yaranta Hindu
Abuja ita ma dana ta yaran Barira ma
anan Gomben take dan ita basu da nisa da
gidan iyayan nasu maza ne ya ce, su yi
karatu, duk anan gida Nigeria dan bai
yarda ya tura dansa wata uwa duniya da
sunan karatu ba, kuma garin da suka
daurewa sheɗana da duk wata lalata kugu
wanne karatun waɗannan makiya Allah
zasu koyawa yaran da suke son musulmi
ne su da a duk duniya basu da abokin
gabar da ya wuce, musulmi, to wanne
karatu zasu koya masa ban da su wayar
masa kai, ya san ilimin lalata ni wallahi
wannan abin yana damu na rashin sanin.
ciwon kanmu, Nigeria wani bature ko ka
taɓa ganin ya kawo dansa Nigeria ya ce,
94
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ya yi karatu, sai mu da bama kishin kasar
mu zamu ringa jidar ‘ya'yanmu tamkar
gyada muna kaiwa makiyanmu masu
burin ganin sun karmu sun rusa mu, su zamu bawa yaranmu.
Ai wannan damar suke samu su
koyawa yaranmu duk wata sheɗana, sai
sun gama lalata musu tarbiya sannnan
zasu turo mana su dan su zame mana
annoba, su buwaye mu, dan haka Alhaji
Bawa yana daya daga cikin mutane masu
kyamatar tura yaransu karatu waje, gaba
dayansu mazan sun yi karatun su ne a nan
gida Nigeria.
Alhaji Mansir ya yi karatun sane a
Jima'ar A.B'U A.B'U Zariya inda ya yi
karatunsa akan kasuwanci wato Business.
Mansir ya dade bai yi aure ba, dan har sai
da dan Auta Isma'il ya fara haɓaka Alhaji
Mansir ya haɗu da Zalifa ne a Misra
95
:
IZGILL JAMILA MUHAMMED
lokacin ya ji kan wasu harkoki da suka
kai shi Zalifa balarabiya ce, gaba da baya
mahaifinta shi ne Wazirin Sarkin na
Misra.
Mansir ya haɗu da Zalifa ne ta
sanadiyar 'ya'yanta wanda Allah ya haɗa
su anan garin Kamfanin Babanta ya je,
domin gogewa da sanin makamar aiki,
domin ya fada har kar Kwangila to wata
rana ne shi ya yanta Alhaji bashir ya
gaiyace, shi cin abinci gidansa to sai Akai
sa'a Zalifan ta je gidan yayan nata ita da
kanwarta Nadiya, tun daga sannan
soyayya mai karfi ta shiga tsakaninsu
ansha fama kafin kasancewarsu
matsayin ma'aurata, saboda iyayanta
basa son tai musu nisa dagewarta ce, tasa
iyayen suka hakura suka aura mata
wanda take so batare da ɓata lokaci ba
aka sha biki amarya ta tare a Nigeriya
a
96
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kuma a garin ‘iyayan mijinta watan
Gombe da farko iyayansa da yan uwansa
duk suna son ta amma daga baya duk sai
suka canja canja mata su ka bi suka
tsangwameta ta kuma rasa dalili sai daga
baya ta gane kan rashin haihuwar da bata
yi bane, a zuciyarta tai mamaki shekara
uku ne kawai da auran su shi ne har ake
gwada mata tsana irin wannan ta shiga
tsananin damuwa ta yadda dangin miji
suke tsangwamarta suka mai da ita
mujiya a cikinsu, duk ta bi ta rame, sai
hanci da manyan idanuwanta da suka
karayin manya idanuwanta da suka
karayin waje, gaskiya Zalifa kyakkyawa
ce dan ko cikin larabawan ma ita din mai
kyau ce, amma duk irin abinda suke mata
bata taɓa gayawa mijinta ba sai dai ko
yaushe ya nai mata korafin ramar da take
yi, ta yi yawa, to dole ne ta rame babu
97
IZGILI JAMILA MUHAMMED
'yan uwa akusa dangin mijin da take san
su zama 'yan uwanta sun tsaneta basa son
ta idan ta je inda suke suna kyararta ai
dole ta shiga wani yanayi to abin Allah
shekararsu biyar da aure Allah ya bawa
zalifa ciki wai murna a gurin Mansir da
Zalifa ba'a magana har ma da dangin
nasa da suke kinta sai duk suka saki aka
shiga tarairayarta, shi Alhaji mansir Bawa
ya yi mutukar murna da Allah ya nufeshi
da ganin jika, daga Mansir da yake
Mansir yaro ne mai hankali da biyayya ga
taimakon marasa karfi.
Akwana a tashi har Allah ya sauki
Zalifa lafiya ta haifi danta namiji
wowowo fadin kyau ɓata baki ne vare.
daka ganshi kasan jinin larabawa ne,
saboda tsantsar kyaunsa duk wanda ya zo
barka sai ya tafi da zancen yaron nan,
Hmm! Zo ka ga bakin Alhaji Mansir yaki
ng
IZGILI JAMILA MUHAMMED
rufawa sai Hidima yake ya kawo wannan
ya kawo wancan dangin Zalifa ma ba a
barsu a baya ba, ana igobe suna suma
suka diro nigeria dauke da kwaryakwaryar kayan arziki dan danginta sun zo
da dama, dan jirgi sukutum kakan ya