eman kudi, ga kuma
iyali, dan ba karamar wahala na sha ba
kafin Allah ya datar dani, na samu
wannan aikin dan haka dan Allah Baba ka
yi hakuri kuma ka dinga kiyayewa abinda
zai ja ya ci mutuncinka, tun da shi baya
ganin mutunci da kima hade da darajar
talaka ba.
Baba ya ce, "Kada ka damu insha
Allahu haka ba zata sake kasancewa ba,
zan kiyaye, tunda abin babu mutunci sai
kai ka alkinta girmanka dan kada a sake
ci maka mutunci.'
95
80
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Malam Sale ya ce, "Wannan
gaskiya ne dole ne ka dinga kiyaye
abinda zai sa a wulakanta ka."
******
Dan audu ne yake ta faman korawa
Alhaji Umar mai da akwai tare da abokin
nasa labari. Fuskar alhaji Mansir ta cika
da annuri ya godewa Allah tunda ya
taimaka aka samu gidan dashi har ya
shiga damuwa da yasa yaji shiru bai sake
ganinta ba, kuma ya ji dadin yadda Dan
Audu ya bincika ya gama cika shi haka
nan Allah yasa ka masa kaunarta tun
ganin daya ke ta mafarki yana yawan
ganinsa yana zaune a wani dokar daji ya
nata kuka shi kaɗai sai ya ganta ta zo
tana bashi hakuri tana lallashinsa duk da
baya ganin fuskarta wani sa in kuma sai
ya ganshi yana cikin fain ciki yana ta yin
mrmushin amma ita tana kuka shiya sa ta
81
IZGILI JAMILA MUHAMMED
tsananta da addu'a ya kuma sa'a taya shi
saukar karatu duk juma'a akan dai Allah
ya tabbatar da Alkhairi idan ita ce, mafi
alkhairi ya kuma kawo sauki ciki lamarin
ya kade fitina dake cikin al'amarin.
Dan Audu ganin irin tarin fara'ar
dake fuskar alhajin yasa ya kara kaimi
yana kara koro wasu kuskuren zancen
duk dai akokarinsa na ganin Alhaji yaga
kokarinsa
aikinnasa.
hade da kwazansa akan
Aikuwa kwalliya ta biya kudin
sabulu dan kuwa Alhaji ya yi masa
kyauta ta mu samman ya yinda Alhaji ya
ce, tukukaicin ka ka gobe ka jira zai a
kawo maka mashin shi ne tukuicin
binciko min gidansu, da ka yi ya kuma
dantso kudin da bai tsaya kirgawa ba ya
ce, "Wannan kuma kasha ruwa ka ji,
ladan kyakkyawan labarin.
82
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Dan audu tamkar zai shiɗe saboda
murna godiya yake gami da jero dogayan
addu'o'in tamkar wani saban maroki,
yana karkawa yayi durkoso a gabansa
yana faman jinjina masa hannu tamkar
yanda akewa sarakai.
Alhaji Mansir ya ce, "To dan Audu
sai gobe ke nan. "
Ya ce, "To ya alhaj."
Alhaji ya fita yana kwararowa
‘ya'yan har jikoki dama tattaɓa kunnan
alhaji kasan zuciyarsa yana ta kakkabin
halin kwarai irin na wannan alhajin shi
sam ba matsolo bane tamkar uban gidan
nasa, da bai ajiye komai ba sai shegiyar
rowa ta bala'i duk yanda kake da shi
babbar kyautarsa ita ce, ya bawa mutum
gudar dubu ɗaya, to lallai wata dakwalar
budurwa ko bazawara ya kawo masa
labarinta to kuwa zai samu gudar dubu ko
83
1
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kuma yinin ya yi yana wahalta masa, to
idan ba daya daga cikin wannan ba ne to
tsakaninsa da kai dari biyu ne sai kuwa
idan yasan kanai masa wata ranar ne.
Zai iya baka dari biyar shi ba abin
kunya bane ka zo neman taimako gurinsa
amatsayinka na yaransa ko kuma dan
uwansa ya tattakura ya fito da naira
hamsin ya ce, a sai wa yara garin rogo
(kwaki)
Duk unguwar Koki babu wanda bai
sanshi ba, koda karamin yaro ne, ka
tambaye shi gidan Alhaji Umar mai
akwai to zai nuna maka sai fa in mai shan
nono ne.
Kowa yasanshi saboda tsabar son
kudinsa da matsolancinsa uwa uba kin
talaka ya ce, talaka ba shi da wani alfanu
a gurin mai akwai. (Wato mai kudi) face,
hidim ta masa shi kuma ya biya shi shi ne
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kawai amfanin talaka a gurin mai akwai,
alhaji Umar mai akwai ya yi mutukar
tsanar talaka gani yake tamkar shi
mutumin shi ya ɗorawa kansa talauci ba
Allah ba, Alhaji Umar mai akwai
shaharar ran mai auri saki ne gaba ɗaya
kudinsa suna tafiya ne aa gurin aure
aurensa mutane da dama sun ce auran
dandano yake ga shi kuma baya san
'ya'yan abin Allah sai ya yo shi daga
cikin masu rabon samun 'ya'ya, ko ya ya
taɓa mace, sai ta samu rabo da shi kuma
abinda yake ba kanta masa ke nan.
Shi fa gani yake a duk duniya babu
babbar matsalar irin zama da mace ɗaya
yasha yiwa abokansa fada idan yana jin
suna fadin matarsu daya ta ishe su ya
kance ba kuda hankali ba kusan ciwon
kanku ba, in banda rashin sanin me
duniya take ciki, ya za ka zauna da mace,
85
IZGILI JAMILA MUHAMMED
daya sai kace jaraba aini ko mata huɗu ba
zan iya zubewa ba in yi shekara dasu
batare da na yi can ji ba, ai gara adinga yi
ana sabuntawa, aikuwa Alhaji Umar mai
akwai ya auri mata kusan ashirin da uku,
a kun dade da shi kina iya masa so sai
shi ne zai barki ki yi shekara, to daga nan
zai ɗaga miki jan kati idan ciki ne dake
zai ce ya bar miki abinda yake cikinki
duniya da lahira kada ki kuskura ki doso
shi da wata matsala ta dan zai kuma yi
miki ba, razanar ranku daga ke har yaran
in dai kika kuskura kika danganta shi da
wata matsala ta yaran zai kuma gaya miki
zai fara rufawa yaran asiri, dan kada ai
masa gorin ko yaran shege ne zai kuma
gaya miki yana nan a amaṭsayinsa na
u