NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 12 of 22

an aikinka ba ko kuma dan ka koshi zaka nuna halin naku na talakawa, daga kunci abinci sai ku ɓollo da salo na rashin mutunci. Baba Audu babu abinda yake in banda makyarkyata yana durkushe yana bawa ubangidan nashi hakuri tamkar zugashi yake, sai faman tujara yake yi masa da tozarci, kala-kala, tsohon zai baka tausayi mutuka saboda a kalla ba a kasara ba zai yi jika da shi, sai wulakanci yake yi masa, irin na zafin naman nan. Hisham ya ci gaba da yarfa ruwan rashin mutunci yace, "Saboda tsabar ka isa tun jiya abaka dakardu ka bani dan. tsabar raini kaki bani har sai da mutumin yayo min waya saboda ya ji shiru, sam baka da niyar bani, saboda ka fara farfaɗowa daga cutar talauci, data kama ka, yanzu kana jin aljihunka da nauyi shi 74 IZGILI JAMILA MUHAMMED ne kake ganin dai-dai kake da kowa tsiyar talaka ke nan, a ɗaukeshi ranga ranga a taimake shi daya fara koshi kai zai farayiwa rashin mutunci, shi yasa ni da talaka babu wani tausayi, ban ɗauki talaka a bakin komai ba, face, kaskantaccen bawa, wanda zai min bauta in biya shi, a duniya babu wata rana da talaka yake da ita, bashi kuma da wani amfani daya wuce mai kudi ya bautar dashi domin shi bawansa ne.' " Shi dai Baba Audu in ban da ban hakuri babu abinda yake yi sai da ya ji ya ɗan tsagaita sannan ya fara bayaninsa ya ce, "Wallahi yallaɓai sanda mutumin nan ya kawo takardun nan ka fita kuma baka sake dawowa ba zuwa kuma sanda ka shigo na manta sai yanzu na tuna, ina shirin kawo maka sai kuma ga ka, amma 75 IZGILI JAMILA MUHAMMED dan Allah dan Annabi ka yi hakuri hakan ba zata sake-faruwa ba, in sha Allahu.' " Cikin Izgilanci gami da wulakanci ya karɓi takardun ya ce, "Kuma daga yau sai yau muddin haka ta kara faruwa to a bakin aikinka, sake kwatanta abinda ka yi, yana nufin ka koshi dai-dai kake da kowa. Dan haka yarage ruwanka, ka kiyaye, ko ka sake, aikatawa. Cikin takunsa na isa hade da kasaita ya bar wajen baba Audu ya dade tsugunne a inda ya barshi saboda tunda yake ba a taɓayi masa wulakanci da kaskanci irin na yau ba, sai kawai ya ji wani irin zazzafan hawaye suna zubo masa ace kamar wannan da yayi jika dashi a ce dan Allah ya yo shi talaka yana aikin a karkashinsa kan ya yi masa laifin da bai taka kara ya karya ba, zai zage 76 IZGILI JAMILA MUHAMMED haka, yana gaya masa irin wadannan maganganun. Ya mike daga durkuson da ya yi yana sharar kwalla cikin mutuwar jiki ya koma kan benci da yake kai dai-dai nan yaji sallama akansa ya dago da sauri yana amsawa Malam Saleh ne direban kamfanin ne ya zauna kusa dashi yana bashi baki ya ce, "Baba ka yi hakuri da abinda yallaɓai ya yi maka tunda Allah ya haɗamu zama dashi babu yadda zamu yi sai dai hakuri shi fa a duk duniya babu wulakantacce a gurinsa kamar talaka, babu wanda yake kyama yake tsangwama hade da kyara irin talaka, gani yake takalmin kafarshi yafi talaka, daraja, a gurinsa ka gan ni nan Baba yallaɓai ba jin kunyar na yi sa'an mahaifinsa baya iya cire hannu ya wanke min fuska da mari. T By lay mida on ideol 77 : IZGILI JAMILA MUHAMMED Baba Audu ya ce, "Me yai zafi malam Saleh?" Malam Saleh ya ce, "Ranar kaddara ce ta hau kaina ya aike ni ne to akan hanyata ne karfan nasara da bashi da tabbas sai kawai mota ta tsaya cak na yi na yi taki ta shi na rasa inda zansa raina dan yaja kunne na in yi sauri mutumin sauri yake zai bar kasar ne, gaba ɗaya hankalina ya gama ta shi kuskuran da na yi na rashin kiransa in gaya masa tun a lokacin kawai sai na fita ina ta 'yan dabaruna ga mi da ‘yan jogane-jogane na, na ma buɗe in jin motar ina ta jagwalgwalawata na bar wayata a cikin mota a she, shi mutumin da ya aike ni gurinsa yana tai masa waya ya ce, ban fa zo ba shi kuma zai yi missin din jirgin shi dan haka shi ya tafi, sai kuma wani lokacin, shi ne shima yallaɓai ya keta 78 IZGILI JAMILA MUHAMMED kiran wayata ina ni ban sani ba, danni ina waje ita wayar tana mota dan haka banji kiran da yake tayimin ba. Sai da akalla na yi kusan awa biyu da wasu 'yan mintoci sannan cikin ikon Allah sai ga shi ta tashi ai cikin sauri na rufeta saboda sai da ya gargade ni da lallai lallai in tabbatar duk yanda zan yi nan da minti arba'in in kasance a gurin, to gashi na kusanyin awa uku aikuwa wanda na je domin sa yama daɗe da tafiya cikin sanyi jiki naja motar na dawo na riga na sani nashi ga wani hali, yau sai Allah aikuwa tunda nai horn aka bude min na ganshi yana ta zirga-zirga tamkar mai nakuda na sanni kuma sai Allah, aikuwa ina tsayawa na fito na durkusa kafin ince wani abu sai jin wani shahararren mari na yi akan kuncina ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba, 79 IZGILI JAMILA MUHAMMED ashe takardun wata kwangila ce zan karɓo masa da yake shirin shakar makudan kudade bana wasa ba, shi ke nan in ba wani ikon Allah ba ya rasa su. A ranar na dandani bakin ciki bana wasa ba wallahi da ina da yadda zan yi da tun a lokacin zan baar aikin nan, to bani da wata hanyar n
🏠