a ce, "Yau ko in ce ma yanzu,
idan kuma kana mamaki ne to ka bude
mana.
"
Ai da sauri Hisham ya cillar da
wayarsa yai bedroom dinsa da gudu
Farida Saraki da Kudurat zaune 'yam
matansa da yake ji dasu dan duk gaba
dayansu ba baya ba, suna iyawa dashi.
Suna kwance akan gado haihuwar
uwarsu da sauri ya daka musu tsawa ya
ce, “Maza ku barmin gidana ga Daddy na
nan ya zo."
Cikin sauri ya zurma jallabiyar da
yake sallah da ita ya bude dirowar gadon
ya dauko kudi kowacce ya bata ya ce,
67
IZGILI JAMILA MUHAMMED
“Sai na neme ku kada wadda tai gigin
zuwa idan ba na kirata ba, yana gama
fadar haka ya ce, Ku fito suka fito sai ya
bude kofar. Kudirat ta saki dariya ta ce,
"Handsome kalle kafa babu pant ana
ganinka a haka zaka je gurin Daddy."
Cikin sauri ya kalli jikinsa ai kuwa
ana ganin nasa kasan cewar rigar ruwan
madara ce kuma tana da yauki mannewa
mutum take da sauri ya fada dakin ya
sako gajeran wando ya fito dai-dai nan
ya sake jin karar wayar ya san mai kiran
batare da ya dauki wayar ba ya bude
kofar yana washe baki daddy ya ce, "Ai
ni da badan maigadinka ya ce, kana nan
ba kuma naga duk motocinka suna nan da
cewa zan yi baka gidan ko kuma ba ka yi
murnar gani na ba my son?"
Hisham ya ce, "Na yi murna mana
daddy.'
68
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Daidai nan suka shigo cikin falon
sosai Daddy ya kallu Kudurat da suke
zaune a falon ya mai da kanshi ga
Hisham din da yake tsaye da alamun
tambaya a fuskarsa, Hisman ya ce,
"Wadannan abokan aikinane wani aiki ne
ya kawosu yanzu.
Suka gaida daddy ya amsa musu
fuska babu walwala su kai waje Hisman
ya buɗe firij ya kawowa Daddy Ruwa da
lemo yana kuma tambayar Mominsa.
Daddy ya ce, "Tana lafiya.”
Daddy ya gyara zama ya ce, “Wai
ni shin Hisham sai yaushe za kai aure ne,
ko yaushe akai maka magana daga kace
wannan sai kace wan can kana ta faman
zille-zille.
Hisham ya ce, “Haba Daddy ni fa
ba girma na yi ba, just 33 year ne fa ka ga
da saura na. وو
69
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Daddy ya ce, "Da sauranka fa tunda
ba kai sittin ba,mana tunda shi ne dai-dai
lokacin ka ko?"
Hisham ya ɓata fuska tabbacin baya
son fadan nan ya ce, "Please Daddy ka
bar maganar nan daga zuwanka ko
hutawa ba ka yi ba, me ake da aure, aure
ai takura ne. "
Daddy ya saki baki yana kallan dan
nasa tun ba yau ba ya daɗe yanayin dana
sanin tura ɗan nashi kasar mai jan kunne
karatu, tun yana tatsitsinsa gaskiya ya
cuci kansa wannan Abu yana damunsa ya
rasa yadda zai yi bai isa yai masa faɗa
akan duk abinda yake yi ba sai ya ce, shi
dai ana san a takura masa, duk ya dauko
dabi'unsu na lalata.
Daddy da idanuwansa suka fara
canja launi saboda ɓacin rai ya ce, "To
wallahi bari in gaya maka in dai ba kai
70
IZGILI JAMILA MUHAMMED
wani abu kan maganar aure ba daga nan
zuwa karshen watan nan tuni zan yi wani
abu a kai, kuma sai na baka mamaki.'
"
Yana gama fadar hakan ya mike
dan yın Alwala dan ya ji masallacin kusa
da gidan suna kiran sallah.
Alhaji Mansir kwangila shi da
Alhaji Umar mai akwai suna zaune a
falon gidan Alhaji Umar din bayan
gaishe-gaishe irin na abokanai, Alhaji
mansir ya ce, "Gaskiya ina cikin
damuwa.?'
Alhaji Umar ya ce, "Ikon Allah
Alhaji me ke damunka Alhaji Mansir ya
furzar da huci mai zafi ya ce, "Akan
yaran wajena Hisham ne, wallahi ina
cikin ɓacin ran kaishi turai karatu banda
karatu har da shedana da duk wata lalata
ta turawa duk ya kwaso, to shi yasa nake
IZGILI JAMILA MUHAMMED
san in yi masa aure, tun lokacin dana
kama shi da giya a firji dinsa nake cikin
damuwa shi yasa nake san yi masa aure
kasan aure abu ne mai girma kuma yana
gyara mutum to gaba daya daya na rasa
yarinyar da zan zaɓa masa mai hankalin
wadda zata juri halinsa ta dinga tuna
masa idan taga yana abunda bai dace ba,
to na yi tunanin na yi tunanin na kasa
zaɓar masa to kawai sai sai
nana tattara
nabarwa Allah lamarinsa ya zaɓa masa
mafi alkhairi na kuma dukufa da addu'a
sosai.
Wani ikon Allah banyi sati da fara
tsaiwar daran nan ba na fara mafarkin
wata yarinya, to amma banga fuskarta
ba, tana sanye da dogon hijabi har kasa ta
juya bayanta da yaro a hannunta to tun
daga lokacin ya zama duk lokacin da na
kwanta sai na yi mafarki, to kwanaki da
72
IZGILI JAMILA MUHAMMED
na zo nan muna magana sai naga wata
yarinya zata wuce Islamiyar."
Alhaji Umar ya ce, Zawuya ke
nan.?"
Alhaji Mansir ya ce, “Ita, ya ci gaba
da cewa "Wato ranar da na ganta sai naga
nutsuwarta da hankalinta nasan ta fito
daga gidan tarbiya shi ne nake san in
tambayeka ko ka san 'yar inace tana saka
nikaf."
Alhaji Umar ya dan yi nazari ya ce,
"Gaskiya ban san ta ba, sai dai akwai
wani yarona kama sanshi dan Audu, to
zan sa shi ya binciko mana in da take da
kuma 'yar gidan waye."
"
Alhaji Mansir ya ce, "To shi ke nan
suka ci gaba da hirarsu akan harkokinsu
da kuma hirar duniya.
Cikin wulakanci ya kalli mai gidan
ya daka masa wata gigitacciyar tsawa ya
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ce; "Saboda tsabar baka s