NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 9 of 16

d suka sake zuwa Sokoto suka hadu da Salim suka je gaishe-gaishen surukai duk wani wanda ya Kaduna suka gaida mahaifiyarta da maigidanta bayan sun koma garuruwansu suka shiga shiryeshiryen biki. Dan ma Baban Salim ya dan kawo musu jinki. Ya ce "Su yi hakuri daga bikin saboda 41 kamata gaishe shi cikin dangin Asma'u sun je masa nan kuma suka rankaya sun masa sami hadawa da na Salim, dan haka duk wani shirye-shirye tsanake su Aminu suka yi binsu, da yake dama tuni Ahmed ya kammala da ginin gidan da Aminun zai zauna cikin 'yan kudaden da Aminu yake turowa ta banki, daga can. Shi ne Ahmed ya gina masa katafaren gida gini na zamani, kuma ya saya masa wata tsadaddiyar mota irin ta tsere sa'a. Salim yana garin Delta yana can yana ta Kirga kwanaki har gani yake kwanakin sun ki gudu.Saboda Salim, Mina ta Ki zaman Kauye ta dawo cikin garin Yola gidan Hajiya Binta Kanwar babanta da yake ta san Salim yana yawan gaisawa. da Hajiya waya domin baya sati guda bai bugo waya gidan ba. Hajiya Bita dai da ta ga son Salim ya yiwa Mina yawa da kanta ta nemi Salim waya ta ce masa "To Salim, Mina fa ta gama idda sai ka san abin da kake ciki." Ai kuwa nan da nan bai jira ba Bata lokaci,_ washe gari sai ga Salim ya dira garin kamar an jehoshi, karo na biyu da suka sake dulmiya soyayya, bayan wancan ta baya. yanzu sun sake dora wata akai duk yanda Salim yake zaton Mina za ta bashi matsala, saboda kunya irin tasu ta fulani amma sai ta bashi mamaki, dan kuwa ya sami hadin kanta ta sake dashi suka yi ta hirar 4) soyayya labari 1T1-1F1 babu wanda basu yi ba, har labarin gidan mijinta da ta fito sada ta bawa Salim.Kwanansa uku Yola suna tare da Mina 'guna soyayya sai da Hajiya ta ga bashi da niyyar tafiya tukunna ta koreshi saboda rashin kunyarsu ta isheta haka nan. Cikin kwanaki uku sun hanata sakewa, dan ko lemo Salim zai sha sai Mina ta cika tambulan ta bashi baki, idan kuwa ita ba ta bashi ba to shi zai ba ta dan haka ya dirkonsu, Hajiya Binta ta fatattaki Salim ta ce ita kam ba za 'al wannan iya-shegen gabanta ba. Kafin Salim ya tafi sai da ya hadawa Mina waya saboda su dinga hira cikin sirri. Dan kuwa -tunda Minah ta yi waya kusan kullum sai sun raba dare suna hirar soyayya, lokuta da dama sai tsakar dare sawu ya dauke yake kiran Mina waya wanl Sa'in ma Sai ya yi barci ya farka, ya kan kirata. Nan da nan Mina ta goge ta fada duniyar soyayya, Sai ka ce ba bafilatanar Kauye ba, wani abin ma in ta yi har mamaki abin yake bawa Salim, satin da ya gabata ya je Sokoto ya sanar da Daddy maganar Mina, Daddy ya ce ya ce "Kar ka damu da yake tuwona maina ne tuni mun gama magana da Baffanka abin da ya rage kawai sati mai zuwa za kai kayan aure, amma mun y! 43 shawara da mahaifiyarka daurin aure kawai za yi, tarewa ba yanzu ba, sai ka Karasa bautar Kasa ka dawo gida sai yi bikin tarewa, ka ga in ka kammala service kai ma za ka fi samun nutsuwa." Salim kamar ya ce "Wayyo Allah!" Don shi sam ba haka ya so ba, to amma kunyar Daddy ta hanashi musu, shi kam da son samu ne kawai yi aure kawo masa matarshi in ya so duk sati ya ke zuwa Weekendgida. Nan take ya yanke shawarar zai lallami Momy akan ta dawo da Mina Sokoto, domin ya san Momi wayayya ce ba za ta hanashi sakewa da matarshi ba, amma muddin Mina tana can komai ya yi Yaddiko Korafi za ta yi ta yi musu ta ce sun yi rashin kunya, sun fita daga al'adar fulani. Kwananshi daya Sokoto ya tafi Kaduna dauko Asma'u, sannan suka biyo ta Kano ya kaita ta gaida mahaifiyar Aminu, lokacin Aminu ba: ya gida da yake ya fara aiki, da wani kamfani na zirga-zirgar jiragen sama, Mama ta yi murna Kwarai da zuwan Asma'u ta dinga ina ka sa ina ka ajiye da ita, ji take kamar ta goyata don Kauna, don ¥3nzu idan ka dauke Aminu Mama ba ta da diyar ad take so zuciyarta kamar Asma'u, babu yadda Mama ba ta yi da su akan su jira Aminu ba, amma Asma'u ta ce sauri suke yi, saboda suna kan hanya. Mama ta matsa akan sai an kai Asma'u ta gano sabon gidan da aka ginawa Aminu,w anda zasu zauna, amma sabo da kunya irin ta Asma'u Kin zuwa ta yi, sai Salim aka raka ya gano gidan. Anan gidan Mama ta zauna yaje ya dawo, sannan suka yi sallama da Mama, suka dauki hanyar Sokoto. Mama ta yi farin ciki da kyautar tsarabar da Hajiya Hadiza ta aiko mata na Umra, dan wannan shi ne karo na farko da zasu Kulla kyakkyawar alaKa. Tun da suka tafi hanya Salim in ban da labarin sabon gidan Aminu babu abin da yake bawa Asma'u dan gaskiya gidan ya burgeshi sosai da sosai. Gidan ya hadu haduwa ma ta Karshe, tun daga kan ginin har irin tsarin furnitures din da aka shirya dakunan, komai ya yi kyau, ya yi tsari hatta kafet da labulaye an zuba wadanda suka dace da tsarin gidan babu abin da zai f: mutum burge sai tsarin babban falo nasu sai ka ce 'Tura, duk yanda Salim ya ke kuranta gidan 'Aminu ita Asma'u duk wannan Kyale-Kyalen sam bai dameta ba, ita burinta kawai ta ganta tare da Aminunta sun zama ma'aurata sun isa Sokoto da marece saboda tsabar gajya, duk Asma'u sai ta ji jikinta babu dadi gala6
🏠