a wasu watanni?
"Amma dai kin sani wancan lokutan bamu da damar auren juna, yanzu kuwa babu wata miskila muna da damar yin hakan ya kamata mu yi amfani da damar da muka samu mu hanzarta yin aure, dan mu mallaki
junanmu hankalinmu ya
kwanta, kin ga sannan zamu gane waye ya fi son wani cikinmu." Ta dan Kura masa ido "Kenan kana shakkun
son da nake yi ma?"
"No ba haka bane Mamace take gardamar cewa son da nake yi miki ya fi wanda kike min to
sai gashi kuma da na zo gidanku Goggo tana Korafin wai Kaunarki ta fi tawa, gashi nan sona zai
illata ki." Ta saki
'yar dariya tana dubansa "Tunda abin
zama mujadala ai sai nemo musu alKalanmu Ahmed da Zaliha ko Salim su zasu raba
gardama. Ya Kura mata ido yayin da ya mayar da maganar wasa "Don Allah don Annabi Asma'u ki yi min alfarma guda daya?" "Wacce iri?" Ta buXata hanzarce.
32
ae rn neil
"Ki amince da aurenmu yi cikin mako biyu zuwa uku, walldhi mahaifiyata ta damu
Kwarai da halin da nake ciki. Yanzu ma jira take
na je mata da KwakKwaran bayani. Haba Asma'u
ai ko ban fada ba kin san ina son ki, son da ya wuce tunanin duk wani mai tunani, ina Kaunarki Kaunar da ta wuce kwatancen mai kwatance ko
kina shakka akan hakan?" Ta dan girgiza "Kai ni ban taba shakka akan
hakan ba." "To idan kuwa haka ne me zai hana aurenmu wannan lokacin tunda muna son junanmu bamu
da haufi akan Kaunar da mu kewa juna tunda har mun yarda da kanmu dan me ya sa zamu tsaya muna azabtar da zuciyoyinmu? Ko ke kina ganin
idan muka dauki dogon lokaci bamu mallaki juna
ba ba zamu cutu ba? Ke tunaniki in wani ya
cutu cikinmu mun yiwa soyayyarmu adalci kenan?" Ta yi shiru yayin da ta nisa cikin tunani. Aminu ya fiddo wayarshi ya kira lambar mahaifiyarshi, bayan ya gaishe ta cikm
girmamawa suka fara tattaunawa. Ta ce "Abba in ce dai yarinyar nan ba ta ba ka matsala ba?" Ya yi murmushi "Wallahi Mama ki kwantar
33
-_
da hankalinki babu wata matsala, Asma'u ta kusan
zama tawa ba ki ji ni cikin nishadi ba. Yanzu ma muna tare, ba abin da yake zukatanmu sai farin
ciki da annashuwa, ga ta nan Mama don Allah ki yi mata addu'a irin wacce kike yi min." Ya mikawa Asma'u wayar, sai da ta dan rusuna
sannan suka gaisa da Mama ta ce. "Haba diyata Asma'u ya kamata ki rinKa jin
tausayin mutumin naki, ki dan rangwanta masa nima tausayi yake bani. Cikin dariya ta ce "Shi kenan Mama ki yi hakuri na tuba, ba zan sake ba."
Ita ma ta yi dariya "To Asma'u yanzu mene ne magana game da aurenku? Sai da ta yi dan dam! Sannan kunya ce ta
ce "Mama ai magana na hannunki sai yanda ki ka
ce dan ni ko gobe ki ka ce daura aure shi kenan. Ta yi 'yar dariya "Shi kenan diyata na gode,
tun da kika hani wuKa da nama in sha Allahu nan da sati biyu ma kin zama amarya. Suka yi dariya gaba daya, sannan suka yi sallama, ta ajiye wayar. Ya juyo ya dan dubeta
tare da sakar mata wani shegen murmushi "Iye
«vaya ga amarya?"
Ita ma murmushi kawai ta yi, wayarta ta
34
dade tana Kara amma ko kula ta ba ta yi ba, har ta gaji ta katse, hirarsu kawai suke mai dadi, dan haka ba ta so wani abu ya katse musu hirar. Amma ko da ta ga an sake bugowa sai ta dauka
tana ganin Salim ne ta kara kunne "Hello sorry please wallahi Salim ban san kai ba ne." Cikin dariya ya ce "Ku ji ni da mutane, wai shin ina ku ka shiga haka?" Ta saki
'yar dariya "Tun da baka san inda muke ba to buri in gaya maka, muna nan garin masoya." "Wai me kuke ne?"
"Soyayya mana." Gaba daya suka kwashe da dariya. Aminu ya
amshi wayar ya ce "Haba Malam kar Ka fa takura mana da yawan kira, kama zuwa Yola mun fasa ba zamu'ba." Ya ce "Ayya komai za ku fada ku yi ku gama
za ka dawo hannu nan gaba sai ka durkusa min, ba kana son ganin Asma''u, ina so ka sanar da ita
cewa maraki fa ba abokin tafiya ba ne." Cikin dariya ya ce "Ahaf, shime kake kafin
lokacin da zan durkusa maka ai ni kuma ina garin
angwaye." "A haba da Allah kun ma isa ai duk gaggawarku dole ma ku jirana..."
"Kai ina ana maganar sati biyu yaushe zamu
tsimayi mai watanni biyu, gaskiya ba zai yiwu
ba." Asma'u ta fizge, ta katse layin "Manta dashi damunmu yake son yi."
"Ba ruwana idan na tafi ke zai tsiya."
Jimawa aka sake bugowa, Aminu ya dauka. Satm din ne dai Sorryplease ku daure ku dawo da wurl, ma nan gidan Goggo ina jiranku da Allah wata unguwa nake son ka rakani. Idan ka biyewa Asma'u ba za ta bar ka ka taho ba." Cikin murmushi ya ce "Shi kenan kar ka damu ga maw nan akan hanya." Yajuya ga Asma'v ne ya ke so mu fita yawo, dan Allah
ki yi hakuri ma koma gida yana can yana jirana, kia san Salim ya fi Karfin komai gurina. Wallahi Asma'a dalilinki ina Kaunar Salim sosai, in baya ga Ahmed babu wanda ya wuce Salim gurina. Suna isa gida suka tarar Salim yana zaman
jixansu yana gaban Goggo suna tattaunawa. Kaya
ne tule falon Goggo wanda Salim ya zo da gaba daya tsarabar Turai ce, wanda Aminu ya
yiwa Asma'u, bayan Salim ya nunnuna mata ta dan girgiza kai gami da kallon Aminu.
"Gaskiya kar ka sake yi min hidima irin wannan, ni kai nake so ba wai abin hannunka ba,
ka gane? Don haka bana so