lin
Asma'u, in ban da ina tsoro kar rabo ya kashe ni da na roki Allah ya cire maka son wannan
varinya, wannan abu ya isa haka nan." Ya dan yi murmushi "Mama ho, ke da na ke
so ki dan gyara al'amarin kuma kawai sai ki yi
fushi in ban da abin ki Mama in ban so Asma'u ba wa zan so. yarinyar da ta Ki mazan duniya saboda ni." Ta ce "To in haka ne ai sai ta aureka.
"Ke dai ki kwantar da hankalinki Mama in
sha Allahu zamu daidaita, aure kamar an yi an
gama. Ba dai na zo Kasar ba, amma don Allah Mama kar ki dinga jin haushin Asma'u wallahi ba
ta wahalar miki da da ba." Mama ta yi dariya "Tun da son ta ya rufe maka ido ai ba za ka ga wahalar ba, in dai ba ta so
in tsaneta to wallahi ta tausayawa rayuwar dana." Shima ya yi dariya "Shi kenan Mama zan
gaya mata." Daga nan suka saki hirar Asma'u suka shiga wata hirar. Ta ce "Wai shin yaushe
zamu tattauna
ye
15
maganar gadonka? Don tun da ka zo ba ka sami
zama ba, bare yi maka bayani ka san dai mahaifinka ya mutu ya bar dukiya da yawa, yana
da kyau ka san kadarorin da ka mallaka." Ya ce "Mama bari tukun sai na sami nutsuwa, duk zan duba takardun kudadenmu na
banki ma bana so fara taba su tunda na zo da
isassun kudade, ni dai Mama yanzu
abin da yake
gabana auren Asma'u kuma sannan ina so ki yi min bincike mu ji ko mene ne dalilin Kiyayyar da
ke tsakanin mahaifina da Baban Asma'u? Dan
tarihi ya nuna da can abokaine." Mama ta yi murmushi "Kwarai kuwa dan ni
"Alhaji Haladu abokin Babanka duk ya gayan
-komai wai da abokaine suna zaman mutunci, shi ne matar da babanka ya aura ta fari zama ya Ki dadi yana sakinta sai shi kuma ya aureta, to
gidan na sama ba ta zauna ba auren bai je ko ina
ba ya lalace, dama can an ce 'yar cc, bo.y "al
zaman aure ta zo yi ba, duk yaudararsu ta dinga y1 dan ta rabasu da abin hannunsu, daga Karshe ta
tatikesu ta gudu, ta bar su da gaba, hakan ya sa Suka ci gaba da Kiyayya da gaba tsakaninsu har
sat da ta kai Alhaji
.Masa'ud ya yi sanadin da Babanka ya rasa kwangilolin da yake samu
hannun gwamnati, nan fa Albaji naka va dave da
tsananta adawa ya yi kutu-kutu sai da ya yj sanadin da Alhaji Masa'u ya rasa kujerarsa ta aiki, kuma lokacin babban Kusa ne na gwamnati kuma daga baya aikin da ya samu bai kama Kafar wancan ba, wadannan abubuwa duk su suka hadu
suka rura wutar rikici tsakanin gidajen biyu har aka auroni, haka na taddasu suna gaba, gashi har na haifeka ka girma basu daina nunawa juna Kiyayya ba, ni dai Babanka har ya mutu bai taba gaya min musabbabin gabarsu da Baban yarinyar nan ba, sai bayan ya rasu amininsa ya warware mun bakin zaren." Sai da ta gama bawa danta labarin abin da ta
sani, ya dan jinjina kai cike da mamaki amma
sam bai wani damn ba, "Allah ya kyauta." ya ce
"Tun da su sun shude suna Kiyayya mu kuma
zamu kafu soyayya, shi kenan kin ga mun wanke musu gabar da suka yi doron Kasa, ai ni wannan labari ya yi min dadi ko ba komai ina da abin fadawa Asma'u, kuma na san dole ta saurare
Ta yi dariya "Kai yanzu dan sokonci sai ka
sami yarinyar mutane ka ba ta labarin abin
ubanta ya yi?"
"To Mama ai ba wani abu bane, tunda komai
ya riga ya wuce amma yarinyar
tana da tsattsauran
10
-_,ra'ayi wai yanzu matsalar ta saboda wani alKawari da ta yi gaban Babana kafin ya mutu, cewa har abada ba za ta aureni ba..." "Oh yanzu alKawarin kenan take son cikawa, shi ya sa ta hargitsa min kai?" "A haba da Allah ta ma isa ai ba zai yiwu ta
cika alKawarin ba, sai dai ta yi azumin kaffara.
rT
Ta ce "To idan ta ji haushin abin da Babanka
ya yi mata kai ma me ye ubanta bai yi maka ba?"
"Mama aj komai ya wuce kar ma tsaya
tashina."" Daga nan ya mike "Bari dai in je
1D yi wanka,
in dan kwanta in huta."" Yana fita daga falon Mama ya fiddo waya aljihu ya lalubi
lambar Asma'u, ya latsa yana jin ta fara ringin murna ta kamashi amma kuma jim kadan sai ya ji
i.ta katse layin haka ya yi ta ty da ta daukasai ta
katse, daga bisani da ta gaji da naci sai ta rufe wayar gaba daya cikin jin haushi ya ja tsaki yana
shiga dakinsa ya cilla wayarshi kan gado, sannan
ya kwabe kayan jikinsa, ya shiga wanka, shi kansa bai san awoyin da ya diba cikin kwamin Wwankan ba, in ban da 7a7zafan tunanin yarinya
guda daya babu abin da yake cikin ruwan wankan. Sai da ya dawo hayyacinshi ya tuna da maganar Mama kada fa da gaske yarinyar nan ta haukata ni, ya fada ransa.
Cikin kwanaki hudu Aminu ya ci gaba da harkokinsa gaba daya ya saki ransa, ya Boye damuwar dake zuciyarsa dan kar mahaifiyarshi ta gane ta tsani Asma'u, amma abin mamaki daga bava Maman ce ta fara matsa masa wai lallai sai va koma Sokoto ya dada rarrashin Asma'u. Ya ce "Ki bar ta kawai Mama ba zan je garin
ba sai an dauki tsawon lokaci ai so ba Karya ba ne, sai ta j1 jiki." Asma'u dai tunda su Aminu suka baro
Sokoto ta kasa samun sukuni ta zama sai ka ce wata mara !afiya koma: take cikin tunanin Aminu take gashi abin da ta yi masa duk yadawo
y2 dameta, to ita in ta ce Aminu za ta aura ya ya
za ta yi da alkawanin da ta riga ta dauka baya, nm gaban Marigay) Alhaji G