NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 14 of 16

arewarta ta ture gwamnatin Aminu ta zama ita ce yar lele,yar gaban goshin Mama, so na duniya babu irin wanda uwar Aminu ba ta nunawa Asma'u ba. To bare kuma yanzu da take dauke da cikin jikanta. Aminu sam bai ji dadin yanda'Asma'u ta tare gidan Mama ba, domin duk yanda ya so ya sake da matarsa yana jin kunyar mahaifiyarshi, gashi ya yi iya Jallami akan su koma gida amma Asma'u 64 ta Ki yarda wai ita sai ta huta, saboda ta san muddin suka koma gidansu fitinarsa ba za ta bar ta ta sami hutun da take buKata ba. Musamman gashi gidan Mama tana samun wadataccen barci da daddare, ga tattali da gatan da take nuna mata. Ta yi shagwa6a soon ranta in ta ga dama ma cinyar Mama take barci, idan gidanta ne da zarar Aminu ya fita wurin aiki ba ta da wanda zata yiwa shagwaba gidan, daga ita sai mai aikinta sai kuma mai gadi. Kwanan Asma'u hudu Aminu ya ji ba zai jure ba dan kewar matarsa ta dameshi musamman makwancinsu ko barci ba ya ityawa, domin yanda Asma'u ta yi masa sabo mai wahala. Aminu dai ya je har gidan Mama ya dauki matarshi ya kai ta gidan Ahmed don ta gano Wasila matar Ahmed da dansu Khalifa, anan suka hadu da Ahmed da Amin har da Wasila- suka yi ta rarrashinta akan ta tausayawa mijinta ta koma gida.Asma'u ta ce "Shin me ku ke so na gaya wa Mama bayan na riga na ce mako biyu zan yi gidanta?" Anan Ahmed ya shirya mata dabara don haka tana komawa gida ta yiwa Mama Karya ta ce "Rijistar da suka yi kwanan baya KarKashin 65 fungiyar manyan likitoci yanzu an fara neman su zasu yi course na makonni biyu." Mama ta ce "Tun da haka ne sai ki koma gida saboda Abba ya sami rangwamen kaiki da daukoki." Dare na yi Aminu ya zo ya tafi da matarsa, daga nan suka sake bude sabon shafi na rayuwa. Haka dai rayuwar wadannan ma'aurata ta kasance cikin soyayya da Kauna da kulawa da juna wannan shekara ne ta kammala karatunta na likitanci cikin nasara, sai dai dan laulayin da take fama dashi, yau da lafiya gobe babu, gashi likitan da yake dubata ya ba ta tabbacin 'ya'ya biyu ne cikinta twins amma kuma duk scanning din da ake jariran suna cikin Koshin lafiya. Satin da ya zo Asma'u ta ji dadin weekend din dan ko manyan bakinta Salim da Mina ne suka zo musu Sallama kafin su wuce Abuja, wani sabon asibiti da Salim zai fara aiki, wanda mahaifinsa ya gina gami da hadin gwiwar wani attajiri amininsa mazaunin Abyja. Asma'u ta yi mamakin yanda Mina ta dawo sai ka ce Balarabiya pashi cikin ya karbcta, ta Kara kvau, ta yi bul-bul da ita sai ka rantse bata taba zaman Kauye ba, gashi abin sha'awa cikinta ba mai laulayi ba. 66 Salim ya dubi cikin Asma'u yana dariya "Gaskiya babynan namu yana wahalar da ke. Amin ya gaya min wai kin daina cin nama, tuwo ne kurum abincin ki. Shi ne nake zaton duk yanda aka yi manomi za ki haifar mana, in ban da manomi ne bebin mu ta ya ya zai hana Mamanshi cin komai sai tuwo." Kwanansu biyu suka wuce Abuja. Watanni suka ci gaba da shudewa, cikin Asma'u na dada girma, har watan haihuwar ta ya kama ranar da ciwon naKuda ya kamata da gaggawa ta dannawa Mama waya ta iso cikin hanzari, suka tafi asibiti, lokacin Aminu baya nan yana can bakin aikinsa ranar jirgi mai zuwa London zai tuKa daga Mama har Asma'u ba wanda ya sanar dashi halin da ake ciki. Suna isa likitansu ne ya karbi haihuwar tata kuma cikin ikon Allah komai ya zo da sauKi, Asma'u ba ta wahala ainun ba. Cikin awanni biyu ta haifi jariranta guda biyu tagwaye. Mama cikin tsananin muma ta rungume 'yan samarin har kuka suka sa ta saboda tuna baya. Bayan Aminu ya dawo gida aka sanar dashi rashin lafiyar Asma'u. kidime ya garzaya zuwa asibitin, amma abin farin ciki yana isa sai ya tadda 'yan jariransa gado suna boxing muma dai gurin 67 Amin ba sai an fada ba, ga 'yan jariransu sun fito duniya ga kuma Ma'unsa ta sami lafiya. daren ya yi ta buga waya yana sanar da jama'ar su haihuwar Asma'u. Washe gari Goggo da mahaifiyar Salim suka iso Kano ganin baby. Momy ta kwana daya ta koma yayin da ta bar Goggo gidan Asma'u suna da kwana hudu, Hajiya Hadiza ta iso daga Kaduna tare da tawagarta, wannan shi ne zuwanta na farko gidan diyar tata, tun bayan aurensu ba ta taba zuwa ba, saboda kawaici. ranar ne dai Salim ya iso tare da matarsa da kuma dimbin sayayyar kayan baby mai jegon kanta ya yi mata dinkuna sama da kala goma. Ranar suna an bar wajariran sunansu Hassan Ca Hussaini, gaskiya bikin sunan ya yi armashi 9sai, kusan duk danginsu sun sami halattar sunan 'yan tagwayen 'yan uwansu na Sokoto da na Kano dana Kaduna duk sun zo, hatta 'yan uwan Salim ba barsu baya ba, dalilin zumuncin da ke tsakanin Salim da Asma'u kowa ya ga irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsu abin ya kan bawa mutane sha'awa, gashi dai duk sun. yi aure amma zumunc! bai yanke ba, an dai yi taron suna an gama lafiya, duk mutane sun koma garuruwansu. 68 Goggo kakar Asma'u ita ce ta zauna gidan mai jegon, saboda kula da jariran, yayin da Mama ta kawo musu mai reno. Haka gaba dayansu suka maida hankali ga kula da jariran Asma'u Allab
🏠