ce dake duniya
irin Kauna da zumuncin da kika nuna min
ai ya isa." Suka yi murmushi gaba daya, Zaliha ta ce "Ni kuwa ina Ahmed abokin sahibin naki kina jin
labarinsa?" "I to idan na so gaisheshi lokaci-lokaci na kan biya
na buga masa waya business center, mu gaisa don
bana so ya san lambata, kin san ni lambar wayata sirri ce, babu wanda ya santa daga ke sai mahaifiyata sai 2.
kuma wanda ya hada min ita amma duk ran da want ya
Zaliha ta yi dariya "Kai ba ki da kyau mutuntiyata,
wanda zan kira sai na Boye
lamba."
"Amma bai dace ki Boyewa Ahmed lambar ki ba domin kuwa Ahmed ya cancanci aboki na Kwarai ga masoyinki Aminu, kin san duk garin nan bashi da
aminin da ya fishi."
"Na san da haka Zaliha, to amma idan na
bawa Ahmed lambar wayata babu abin da zai hana Aminu ya
dinga kirana waya,
idan kuwa haka ta kasance ba
Karamin rudani zan shiga ba, kin sani jin muryar Aminu
za ta 1ya hankatani haka sauraren lafazinsa, zai haddasa min rashin kwanciyar hankali, na jima da dafin soyayyar da ya riga ya watsa min cikin rai, ya tafi ya bar ni
ganta ranar zan sauya layi."
lambar ta ki ma ba kya so gani?" "E, wallahi bana so kowa ya
santa don haka duk
Zuciya na yi min radadi. Da ace fili take babu abin da
zai hana in hukunta zuciyata, amma tun da Boye take
ba ganinta Aminu zan hukunta don haka duk wani mataki da zan dauka akan Aminu da Ahmed kar ku ga
laifina domin Ahmed yana sane da irin halin da na shiga
amma bai yi komai kai ba..." "E to ke ma kin yi magana anan koda yake Aminu
bashi da laifi da yawa, tunda har yanzu bai san aurenki ya mutu ba..."
"Asma'u ta katse ta "Ko bai sani ba me ya hanashi yin bincike domin jin halin da nake ciki? Idan Ahmed ya
Boye masa ai ya dace ya yl yawa ya binciki sauran
abokansa." 27.
eee
Ranar daurin auren Asma'u da Faruk ya kama
ranar Lahadi, dimbin jama'a 'ya uwa ds abokan 'Faruk
tun da sanyin safiya suka rankaya
zuwa Sokoto, motoci da yawa sun yi jerin gwano bimin na Shehu, en daura
aure gidan Kanin mahaifin Asma'u unguwar Rinjin
Sambo Low Cost. Faruk dai ya shirya gagarumin biki domin ya yi niyyar za yi shagulgula na kece-raini dan ko ya yi alkawari sai naira ta sha kashi wurin bikinsa da Asma'u musamman da yake yana gani shi aurene na fari gurinsa, don kuwa Faruk matashin saurayi ne bai taba
aure ba, sai akan Asma'y zai yi auren fari, shi ya sa ya
ke ta rawar kai da zirkilli dan ko ba komai dai shi ganinsa ya tsere sa'a tun da ya yi nasarar auren Asma'u
kyakkyawar yarinyar da ta girgiza 'yan maza amma abin
Kaddara sai abu ya Zo da tsautsayi da yake mu 'yan adam
muna tamu Allah yana taSa, hanyar dawowa daga daurin aure motar angwaye ta yi hatsari kuma abin.. mamaki babu wanda ya ji
rauni sai ango, su hudu ne
cikin motar, amma Faruk shi kadai ne ya ji rauni da yawa don haka suna isowa Kano aka zarce dashi asibiti. Lokacin da aka sanar da Asma'u ba Karamin tashin hankali ta shiga ba, duka gidan haka suka kwana babu
sukunt. Washegari tun da safe ta shirya tana niyyar zuwa asibiti dubo Faruk, sai ga sao daga asibiti Faruk ya
aiko kawo mata wani abokin Faruk din ne ya zo har gida ya kawo mata bayan sun gaisa ya mika mata
(envelope) ta sa hannu ta karba ta yi godiya, sai da ya
tafi ta bude wasikar, amma mamaki ne ya kamata ganin
ba wani abu bane ciki illa takardar saki, wai cewar Faruk ya saketa saboda gudun kar rabon wani ya
kasheshi, dan haka ta yi hakuri tare da yi masa addu'ar Allah ya rage masa sonta zuciyarshi. Kuma sannar. duk abin da ya yi mata ya bar mata kyauta, kar ma ta y.
tunanin za ta maido masa da kayan auren da ya yi mata. Asma'u tana gama karanta takardar ta saki kuka, ta
tafi da gudu ta fada cinyar Goggo "Wayyo ni Goggo na
shiga uku, me na yiwa maza suke Kina, wai shima Faruk
ya sakeni. Ta ci gaba da kuka. Goggo ta rungumeta "Haba Ma'una, mene ne abin
damuwa dan aurenki an sakeki, tun da ba kanki aka
fara saki ba, bare ki zama ta Karshe shin Faruk shi ne
au maza? De har za ki damu kanki, ki tuna kin rasa Aminu ma kin haKura bare wani Faruk." Haka dai Goggo ta yi ta rarrashin Asma'u duk da Asma'u ba son Faruk take yi ba amma sakin ya yi mata
ciwo. Da daddare sam kasa barci ta yi saboda damuwa, daren ta bugawa Alhaji Yahaya waya tana kuka ta sanar dashi mutuwar aurenta ya ce "To Asma'u tunda taurin
kaine dake ya zamu yi dama tun farko abin dana guda
kenan ki yi hakuri yin aure yanzu ba naki bane ki zauna ki
jira Aminu, yaron da kike so shi kadai ne mijinki..." Ba ta tsaya saurarensa ba, ta katse wayar sannan ta sake bugawa Zaliha ta gaya mata Zaliha ta ce "Ni sam ban ji haushi ba, dan Faruk ya ki ki ai ba Aminu ne ya Ki ki
ba, ki tuna fa ba don kina son sa ki ka aureshi ba, hakan ma da ya yi va raba gardama gara da ya
sawwake miki
tun baiwa Aminu 6bama ba, don Faruk ya
sake ki ba wani abin damuwa banc." Cikin kuka ta ce "Amma ai ko ba komai Faruk ya
6atan suna, mutane zasu ke camfani su dinga guduna...' "To mene ne in sun guje ki? Ca nake dai Aminu
kadai kike so, kuma na tabbata duk inda yake yana nan
vana son