arin da take ba, gaba daya hankalinsa
ya ji ya tashi komai ya kwance masa, ji ya yi tamkar ya
yi tsuntsuwa ya taho Najeriya, yanzu kam zaman Turai ya gundireshi in band ya ganshi Kasar shi ta haihuwa babu abin da yake buKata. Gaba daya hankalinshi ya tafi ga
auren Asma'u, shi dai ya ganshi yau gashi ga Asma'u, matsayin ma'aurata shi ne cikar burin rayuwarshi. Nan da nan ya
ajiye aikinshi dan ba zai
jure zama wata Kasa ba, alhali Asma'u na Can Najeriya ba ta da aure, in ya yi haka ma
al ya ci amanar Kaunar da ta nuna masa, dan haka &aggauce ya yi shirin baro Kasar Rasha, ya dire Najeriya Kasarshi. ta gado da zummar neman masoyiyarsa Asma'u duk inda take fadin Najeriya. Kwananshi biyu Kano suka zauna shi da abokinsa Ahmed suka tsara yadda zasu fara neman Asma'u da yake lokacin da ta zo gidan Ahmed ta Ki
fadin takamaiman garin da tek da zama. Aminu ya sanar da mahaifiyarshi zasu je neman
fi
Asma'u. Mamaki ya kama babarshi. "Shin Abba har yanzu yarinyar nan tana ranka?" Ya dan shafa kai yana murmushi "To Mama ya ya
zan yi tun da Allah ya jarrabi zuciyata da Kaunar yarinyar, kawai dai ki yi min addu'a Allah ya yi min
katarin ganinta.
Itama ta yi murmushi "To Abba Allah ya bada
sa'a. Koda yake ina ganin Kila fa yarinyar nan duk inda
take tana da aure, domin lokacin da ta zo gaisheni cewa
ta yi mijinta ne ya kawota. oF
"Kai haba Karya take an gaya min tuni aurenta ya mutu."To ku yanzu ina kuke zaton za ku sameta?" "E to zamu fara zuwa nemanta garin Sokoto idan
bamu sameta ba sai mu nufi Kaduna, inda Mamanta take
"To Allah ya taimakeku ku sameta." "Amin Mama, addu'ar da nake so ki yi mana
kenan. Gobe ne zamu tafi Sokoton." Washe gari sammako suka yi shi da Ahmed suka nufi birnin na Shehu, suna shiga cikin garin Sokoto sai
suka dauki hanyar da za ta kaisu Kauyen (Shodi) da
yake babu wani taKamaiman wurin da zasu nemi Asma'u garin Sokoto, dan haka stka yanke shawarar
zuwa wannan Kauye dan suna zaton akwai wasu
Kakanin Asma'v wannan gari, amma koda suka shiga
sai suka yi ta faman bilinbituwa sam gidan da suke nema
ya Bace musu, suka yi ta yawo cikin Kauyen suna
tambaye-tambaye
sai da suka gaji da yawo duk sun
karade ko ina sannan Allah ya taimakesu suka sami
aure
has wani dattijo ya ce ya san gidan da suke nema. Nan take
ya
rakasu gidan Dudu Kanwar Kakar Asma'u, bayan sun
sami gidan sai suka yi rashin sa'a she ita dai Dudu Allah
ya yi mata rasuwa, tun tuni kuma duk iya kokarinsu
nasu sami koda daya daga cikin ya'yan marigayiyar duk abin ya ci tura, domin dukkansu sun tafi cirani sai da damina suke dawowa gida. Amma koda su Aminu suka matsa da bincike sai aka yi musu kwatancen wani tsoho wani dan Kauye
gaba
kadan aka tabbatar musu in dai suka je gurinsa
zai
gano yarinyar da suke nema, domin shima dan uwan Dudu ne. ~Su Aminu suka yi mura, suka nufi garin da
tsohon yake har da dan rakiyarsu. Bayan sun isa garin
suka je-gidan mutumin suka ggaisa
sannan suka
zayyanewa wannan
tsoho abin da yake tafe dasu, suka
kwatantama masa Asma'u suke nema. nutse suka gabatar da kansu sai da tsohon ya
gama fahimtarsu tsaf kuma ya riga ya gano ko su su waye nan take ya raya ransa wato masifar da ta tafi tun
shekarun baya ita ce take so ta sake dawowa, haka
kawai muna zaune cikin kwanciyar hankali wannan
kafirin yaro ya Zo ya tayar mana da hankali,w ato kenan
so suke duk su karkashemu da wannan shegiyar soyayya
yanda suka kashe uban yarinyar nan. To wallahr ba zai yiwu ba, yanda suka zo haka zasu koma amma ni ba zan
gaya musu inda jikar Yalwa take ba. Su dai su Aminu da suka yi shiru suna jiran amsar da tsoho zai basu amma abin mamaki duk Bata lokacin
da suka yi wajen kwatanta masa Asma'u tashi daya sai
te
ya birkice musu wai shi sam bai gano yarinyar da suke nufi ba, babu mai sunanta cikin danginsu daga Rarshe da suka matsa masa sai ya ce "Ayyo na tuno yarinyar da ku ke nufi, ko ba Ma'u 'yar gidan Marigayi Alhaji Masa''ud na Kano ba?" Da sauri Ahmed ya ce "Yauwa ita muke nufi Baba." Yayin da Aminu muma ta kamashi Allah-Allah
yake ya ji abin da tsohon zai fada, shi dai kawai burinsa ya ji garin da Asma'un take amma budar bakin tsohon nan Sal Cewa ya yi. "Allahu Akbar kaico duniya, ai in dai wannan
yarinyar kuke nufi ta rasu tun tuni wjaen haihuwar
jikar Yalwa ta riga ta mutu da dadewa. Nan da nan Aminu ya dafe kai da hannu biyu cikin
Karaji ya ce "Shi kenan ta faru ta Kare, rayuwata ta
ruguje.Ya tsuguna gaban tsohon yana rasgar kuka sal ka ce Karamin yaro. Tsohon ya ce "Haba samari hakuri za ku yi ai duk mai rai mamaci ne, mu ai tuni muka yi kukanmu muka "FE hakura. Ahmed duk ya riga ya Kule da haushin tsohon nan, ya dafa Aminu "Ka yi hakuri abokina tashi mu tafi kar ka damu duk inda Asma'y take zamu nemota. Aminu ya dan harareshi "Haba Ahmed ya kake
abu kamar wani yaro, kana ji
fa bawan Allahn nan ya ce' mana Asma'u ta mutu, in haka ne ina zamu nemota?" Ahmed ya janyo hannunsa "Ni dai kawai ka tashi mw tafi." Ya juya ga tsohon nan "To Baba dattijo mun
gode Allah ya ji Kan Asma