o ya duba rubutun da take
cikin computer, ya yi 'yar dariya
"Malama likitan nan fa da gaske yake yi ya bugo min waya yanzu ya jaddada min bafatarsa. Ta dan kada ido gami da harararshi "To inda gaske
yake sai me?" "Kai gaskiya yarinyar nan masha Allahu akwai ki da dankaren farin jini, gashi nan maza sai kawo caffa
suke.*
"Haba da Allah sai ka ce ni ce kai ga ka nan 'yan
gusta sai rububinka suke ka tsaya kana yanga sai faman
yankwanasu kake. Cikin murmushi ya ce "Haba yarinya kin dau bashi na data yi miki uzuri daga yanzu duk wanda ya ce yana
sonki zan bashi dama." Ta dan marerece "Haba Yaya Salim mijin Mina, ai hama haka da kai. wannan lokacin Shema'u Kanwar Salim ta shigo
"Anti Asma'y ki zo ki ci abinci in ji Mommy." Salim ya ce "Je ki ki kawo mata nan." Asma'u ta ce "Anya zan ci abincin nan, lemo
kawai za ki kawo min." Salim ya ce "Dame-dame aka yi kicin?" Shema'u ta ce "An tuKa tuwon shinkafa da miyar agushi, kuma akwai shinkafa da salad sannan akwai
70
ragowar farfesu," "Shi kenan abin da aka girka
kicin din?"
"Ina jin shi kenan amma bari dai na tambayo masu
aikin kicin din ko akwai wani abin bayan wannan. Har ta kai bakin Kofar "Ji nan Shema'u." Salim ya
ce da ita "Je ki sa hado mata salad ki taho kuma da
lemo saboda Antin taki ba ta fiye
son cin abinci mai
nauyiba." Asma'u yini guda ta yi gidansu
Salim, sannan da marece ya maida ta gida.
"Yan makarantun jami'a
sun sami hutun Karshen
zangon karatu wanda shi ne Salim ya
kammala
karatunsa fannin likitanci,
ita kuma Asma'u tana shirin
shiga (level three) Kwamishina baban Salim ya
shiryawa dan nashi Kasaitacciyar liyafa
saboda murnar
taya babban dan shi nasarar kammala karatu lafiya, ya
gayyaci manyan mutane da dama. Bayan an gama komai, ya shirya musv tafiya Kasar
Jamus (Germany). Bayan tafiyar su ne Asma'u ta raka su Momi biki can garin Yola burin Asma'u bai wuce ta ga Mina ido da ido ba, ai kuwa suna isa da kwana daya Mina ta zo lokacin da Mommy ta nunawa Asma'u ita ba Karamin firgita ta yi da ganin yarinyar ba, muguwar kyakkyawa ce, sai ka ce aljana, tsananin kyanta ya zarce duk yanda kake zato ita kam duk yanda Salim ya
siffanta mata ita yanzu da ta ganta sai ta ga ta wuce
nan, abin sha'awa Mina tana da fara'a da son jama'a
gashi kuma ta waye, saboda zaman birni da take yi. Hausarta tana fita sosai, amma kuma Asma'u ta ji
labanin wai Mina har yanzu ba ta daina yiwa mijinta
tawaye ba, kullum ita kenan guje-guje gidajen 'yan uwa. Asma'u ba ta fi mako daya da dawowa daga bikin
Yola ba ta yi shirin tafiya Kano wurin bikin Zaliha
Kawarta, tare da gudunmawarta mai tsoka. Lokacin da ta
isa Kano ba gidansu amaryar
ta sauka ba, dan
girmamawa sai ta sauka gidan dan uwan mahaifinta dayake shi kadai ne dan uwansu wanda ya rage garin
Kano, wato mahaifin Yusuf mijin da aka aura mata da
farko, lokacin da aka sanar da Yusuf zuwan Asma'u da
saurinsa ya ZO yi mata sannu da zuwa ganinta ke da wuya duk sai ya rude, saboda irin canje-canjen da ya
gani tare da ita. Asma'un da aka yi musu aure tana Karamar yarinya har yana raina shekarunta, amma yau
gata ta ama munzalin mace sosai, ta goge ta dada wayewa, boko ya ratsata sosai, gashi
idonta ya bude
saboda cudanya da masu ilimi, rayuwar
ta gaba daya ta.
sauya ta samu ci gaba kowanne fanni ta dada kyau
sosai, jikinta ya murje, ta yi haske fatarjikinta sai sheki
take yi. Kuma abin mamaki ta bashi hadin kai suka
gaisa faran-faran cikin mutunci, babu wani alamar raini ko tsiwa. Sai ma girmamashi da ta dinga yi matsayinsa na dan uwanta, sam ta nuna kamar auren dole bai taba
shiga tsakaninsu ba, shi kuma ganin haka sai ya fara bullo mata da maganar kome, wai ta yi hakuri su maida
aurensu tunda yanzu su ba yara bane, sun mallaki hankalinsu. Dariya kawai ta yi ta shareshi, duk yanda ya
so ya shisshige mata ta ki yarda. Da ya matsa mata da
zancen soyayya sai ta ce ya yi haKuri dan yanzu shi
72
Yayanta ne, zai fi kyau su rike matsayinsu na 'yan
uwantaka amma ya fidda batun komai. Ya kada ya raya ta ki bashi goyan baya, ita abin ma dariya ya bata, sai dai kuma ta yi mamakin
shiryuwar da Yusuf ya yi ya
zama nutsattsen mutum, ba
kamar shekarun baya da yake harkar sharholiya ba da alama yanzu duk ya tuba ya daina shaye-shaye
amma
koda ta
tambayeshi labarin abokinsa Bashir, sai ya
shaida mata bashi da lafiya yana nan yana jinya, duk ya
fita daga kamanninsa sakamakon kamuwa da cutar Kanjamau (AIDS) da ya yi. Allah ya kyauta abinda ta ce kenan tun da Asma'u
ta zo biki Yusuf na tare da ita, duk wata zirga-zirgar zuwa gidan biki shi ne ya ke dawainiyar kaita da daukota, fir ta Ki yarda direba ya kaita bayan haka ta
ziyarci mutane da dama har gidan Sunusi abokin Yusuf sai da ta je ya yi aure har da 'ya'yanshi biyu sannan ta je
gidan Ahmed abokin Aminu, babu yanda bai yi da ita
akan ta daure su gaisa da abokinsa waya amma fir ta Ki yarda ta kawo uzirin wei tana da miji, kuma ta Ki yarda
ta kar6i lambar Aminun. Bayan nan ma har. gidan Babar Aminu ta je ta gaisheta, ta kai ma