NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 6 of 13

cin haduwar su ya yi sai ta ji ranta ya yi mugun faci, ta ji kamar ta yi bindiga ta fashe da ta tuna cewa yanzu fa Aminu na can cikin jiranta "Allah sarki masoyina." Ta ambata a ranta. "Sa'o'i biyu da wucewar lokacin da suka saba haduwa, tana kwance a daki Dela na rarrashinta sai ta ji na'urar sadarwarta wadda ke amfani da iska ta dau kara. Kamar ba ta son fauka ta mika hannu ta dauka. Sunan wanda ta ke kauna ne ya fito a kan gilashin na'urar. Da gaggawa ta kai kunnenta. 24 "Aminu...." Ta ambata a maimakon amsawar da aka saba yi "Hello!" Shiru ta ji, hakan ya kuma sawa ta cc. "Aminu, kana ina?" "Ina nan ina jiranki, a wajen da kika shanya ni..." "Wayyo masoyina." Ta runtse idanunta kana ta mike da kyar ta zauna. "Bana jin dadi ne yau." Ya yi shiru na dan lokaci sannan cikin damuwa ya cc. "Ba ki da lafiya, me ya ke damunki?" Ya bukata muryarsa kunshe da damuwa. Ba ta so ya san abin da ya faru a kanta sai ta сс. "Ba komai ma na warke..." "Eh, na ji kin warke, tambayarki na ke me ya sameki? Ta yi shiru tana tunanin abinda za ta ce masa. "Na ce ma na samu sauki." "Ni kuma na ce me ya sameki?" Ya maimaita. Dabara ta fado mata. "Ciwon son ka ne ya kwantar da ni." Ta hada da 'yar dariya. Ya san ba haka abin ya ke ba kawai bata son sanar da shi, don haka sai ya ce. "To yanzu yaushe zamu hadu?" Ta dubi Dela kamar ta ki fada sai ta ce. "Zan yi kokari mu hadu gobe." Allah ya kai mu." Ya ce a sanyaye sannan ya kashe. Har ya kashe wayar tana makale a kunnenta. 25 Se Aminu ya hau ya motarsa koma gida jikinsa a sanyavc. Tunda ya isa gida mahaifiyarsa ta fahimci hakan, wannan ya sa ta nace da tambayarsa ko bashi da lafiya ne? "Lafiya Kalau Momi." Ya ce da ita sa'ar da ta je har daki ta sameshi a kwance. "Lafiyar ka kalau kuma ka zo ka kwanta tun yanzu, da haka ka ke yi?" Ta ce cikin zargin kin fada mata gaskiya. Ya yi shiru bai yi magana ba, hakan ya sa ta kKara tabbatar da zarginta kuma shi ya bata kwarin gwiwar ci gaba da tambayarsa "Wato kai yanzu har akwai abin da za ka iya boye min ko? Ka girma kenan mu ba mu isa komai a wajenka ba." Ya girgiza kai daga kwancen. "To me ka ke nufi da kin fada min abin da ke damunka?" Ba shi da amsa, mafita daya kawai ya sanar mata abinda yake akwai ko wata kila ta iya tallafa masa. Ya dogara hannayensa biyu ya tashi zaune. Ya dubi mahaifiyarsa ya cе. "Momi Baba ne ya cc ba zan auri 'yar gidan Alhaji Masa'ud ba..." Ya yi shiru gami da dukar da kai. Babbar magana dan sanda ya ga gawar soja. Ai ita ma abin ya fi karfin ta. Ta jima tana dubansa duba na tausayawa saboda ya zo da abin da ta san yiwuwarsa 26 tamkar yiwuwar fitowat kaho ne akan jaki. "Abba na." Shi ne sunan da ta ke kiransa da shi saboda sunan mahaifinta gareshi. Ya daga kai ya dubeta gami da amsawa a sanyaye. Kai tsaye ta wuce da cewa "Ka zo da babbar matsala guda daya me matukar sarkakiya, sarkakiyar da warwararta za ta zama gagarumin aiki ja."Ta dan sarara ta ja numfashi sannan ta ci gaba. "Abba ka riga ka san irin dambarwar da ke tsakanin mahaifinka da mahaifin varinyar nan anya ka yi tunani na zabo ta a matsayin matarka ta aure kuwa?" Bata bukatar amsa, don haka ta ci gaba "Ba ka yi tunăni ba kuma lallai ina mai baka shawara da ka sauke wannan nufi naka tun dare bai yi ma ba domin ba za ka yi nasara ba. Ba don komai ba sai don sanin cewa Alhaji Masa'ud makiyinmu ne, ba mai kaunar mu ba ne." Ta yi shiru tana kallonsa. Tuni idanunsa sun fara cikowa da kwalla. Ya daga a hankali ya dubi mahaifiyar tasa duba mai cike da ban tausayi sannan ya се. "Momi ni fa da ke na dogara, ke daya ce na jingina a tunani na a gareki ne kawai zan samu sa'ida" Ya kuma dukar da kai. Tausayin Aminu ya lullube zuciyar Hajiya Sa'ade. A hankali ta taso daga kujerar da take zaune akai ta tako ta zauna a gefen gadon da yake zaune. "Abba." Ta kuma kiran sunansa a sanyaye "Kamar yadda ka ce ni kake tunanin samun nasara ta 27 hanyata wannan haka yake kuma zan iya matuka ga duk abinda kake so don ganin ka mallakeshi, amma ka sani ban da wannan. "Abin da ya sa na ce ma haka shi ne tun sa'ar da na shigo gidan nan na iske wannan matsananciyar gaba ta su ni kaina yanzu idan ka takura ni ban san dalilin yin ta ba." Ta yi shiru, sannan ta ci gaba "Ka yi hakuri Abbana ka nemi wata komai mai wuce wa nc." "Amma ban da son Asama'u." A zuciyarsa ya fada. Amma a zahiri bai ce komai ba. Ta dauke kanta daga kallonsa "Idan kana son wadda zaka aura ne ba-sai lallai Asama'u ba ga yan matan nan barjak a gari. Ka sauya shawara ka ji?" Bai yi wata alama da ta nuna ya yi na'am da zancen mahaifiyar tasa ba haka kuma bai yi mata gardama ba. A haka ta tafi ta bar shi zaune yana ta faman tunani. Karfe biyar na yamma kamar yadda suka saba a can ta vi masa, inda suka saba haduwa. amma shiru har tsawon sa'a guda babu ita babu dalilinta. Ya mike ya kade babbar rigarsa ya nufi motarsa, zuciyarsa cike da zulumin rashin ganin masoyiyarsa tsawon kwana biyu. Lokacin da ya kama
🏠