aúrar wa da 'ya ko ko ya ya, da za ki ce wani
tunda ta taso bata taba gani ba....wannan har wani abin birgewa ne?"
Hadiza ta nisa "Ki yi hakuri Goggo, ni ma ba tsari na bane kin san halin sa...."
"Ba ruwana da wani halinsa, ke ma ai dakc. Me
yasa idan yana yi ba kya kwabarsa? To ni ba zan taba
yarda da wannan ba."
Hadiza ta cira kai ta dube ta. Ba shakka ta
fahimci ran Goggo ya 6aci, wannan kuwa ta san ya biyo
bayan rashin sanin irin zafin da Alhaji ya dauka a
dangane da abin ne. Ta kuma nisawa.
"Allah ya huçi zuciyarki Goggo, nima abin ya fi
karfina ne, don gaskiya da farko ban so hakan ba amma
ganin irin furucin Alhaji yake yi na cewa da ya aurar da
Asama'u -ga dan gidan Alhaji Gambo gwanda yamutu...."
"Eh!" Goggo ta dafe baki "Gwanda ya mutu fa
ya ce?" Ta gyada kai "To kwa zai mutun in dai akan
aure ne. Wa ya fada masa akan aure sunnar ma'aiki ana
yin wannan kalami?" Ta tsagaita "Yanzu yana ina?"
"Ya fita tun dazu." Hadiza ta amsa a sanyaye.
Goggo ta nisa "Na so ace yana nan don na bashi
wani labari na wani mutum da ya yi makamancin irin
wannan faruci don ya san aure ba a hana shi." Tana rufe
baki sai suka ji sallam.
Wanda take nema ne ya shigo da saurinsa.
Mantuwa ya yi don har ya kusan zuwa ofis ya tuna bai
dauki wasu muhimman takardu ba, saboda ya fita yana
fada akan dole sai 'yar sa Asama'u ta rabu da masoyinta
1
Aminu.
Ya yi turus! Ganin mahaifiyarsa, da hanzari ya
durkusa har kasa, ya ce "Sannu da zuwa Goggo....ina
kwana?"
"Lafiya kalau." Ta amsa kamar ba ta so.
"Tashi ka zuana ina son magana da kai dama
yanzu na ke tambayarka aka ce ka fita."
Ya tashi ya zauna jiki a sanyaye.
"Kai me ya sa kakc kokarin raba wannan 'ya da
wanda take so?" Ta kura masa idanu tana jiran jin abin
da zai ce.
"Wacce 'ya kenan?" Ya bukata kansa a duke.
"Wacce 'ya kake da ita yanzu a gidan nan?" Та
mayar masa da tambaya.
Tun farko ya san wadda take nufi amma saboda
sanin cewa zuciyar shi ba zata taba amincewa da aurar
da 'yar sa Asama'u ga dan babban makiyinsa Aminu ba,
shi yasa ya tambaya.
"Ba ka ce komai ba...ba da kai nake ba?" Ta ci
gaba a zafafe ganin ya yi shiru.
In ban da yana shayin Gwaggo da ba abin da zai
hana ya hau ta da fada. Kamar yadda ya ajiye a
zuciyarsa babu mutumin da ya isa ya yi masa wannan
maganar ba tare da ya mayar masa da martani ba. To
amma ita wannan mahaifiyarsa ce, ko ba komai akwai
darajar haihuwa. Abu daya kawai-ya dace ya yi mata shi
ne ya nuna mata yanzu zai je wajen aiki ne jama'a suna
jiransa idan ya taso zai je gida ya samcta, shi kenan ya
huta. Muryarsa a marairace ya cc.
8
"Goggo wannan maganar doguwa ce, ki yi hakuri yanzu ana jirana a wajen aiki..."
"Au Allah.....ana jiranka a wajen aiki wato aikin ya fi maganata kenan ko?"
"Ba haka banc Gwaggo."
"To ya ya ne?"
Ya dukar da kai "Allah ya huci zuciyarki, ina sauraronki."
ma?"
Ta harareshi "Au har ka manta tambayar da na yi
Ya girgiza kai "Ban manta ba. Gwaggo ni kaďai
ne na san abin da ya sa na ki amincewa da wannan
al'amari, saboda..."
"Ka ga Malam dakata bana son dogon turanci.
-Ka gani ka kiyayi kanka da yunkurin tarwatsa hanyar
gina sunnar ma'aiki, idan ba haka ba ba shakka za ka yi
karkon kifi a rayuwar ka. Akwai mutane da dama da
suka bi irin wannan hanya da ka ke shirin bi suka yi
dana-sani. To wai kai menene ma tsakaninka da Alhaji
Gambo da har zaka dauki karan tsana ka dorawa
Tansa?"
Alhaji Masa'ud ya sosa keya cikin rashin sanin
yadda zai ce.
"To ka ga saurareni da kyau ina so ka nutsu don
zan baka labarin wani mutum mai irin wannan hali naka
wanda daga karshe ya yi mummunar makoma, don ka
kiyaye domin an ce in ka ga gemun dan uwanka ya
kama da wuta shafawa naka ruwa." Ta yi shiru.
Alhaji Masa'ud ya matsu kwarai ya tafi wajen
9
aiki amma gudun kar Gwaggo ta ce ya fifita aiki akan
maganar ta sai ya tsaya don jin labarin nata.
"Kana ji ko? Wannan labari da zan baka ya faru
ne a lokacin da na je Maiduguri gidan yayarka."
A unguwar da na zauna an yi wani Alhaji
hamshakin mai kudi mai suna Alhaji Salisu wasu kuma
suna kiransa rumbun naira. Mai kudi ne sosai na gani na
fada, to amma sai aka wayi gari suna matsananciyar
gabar gani a fada da wani makwabncinsa da mafi
yawancin mutane ba su san menene makasudin ta ba. To
amma da tafiya ta yi nisa cikin gama ya gama sai aka
gano dalilin gabar tasu.
Gabar tasu ta samo asaline tun suna samari. Sun
nemi mace daya ne da aure a wancan lokacin wanda 21AD
bayan gwagwamarya da aka yi shi Alhaji Rabo ya yi
nasarar kasa Alhaji Salisu ta hanyar" aure Suwaiba
(matar da suke so su biyu) To tun fa daga wannan gaba
ta kullu sosai abin ya zama ko ga maciji ba sayi a
tsakaninsu.
Suna nan zaune cikin wannan hali na yau fada
gobe masifa bayan shekaru masu yawa sai Ubangiji ya
kulla wani abu a tsakaninsu. Wato dan gidan shi Malam
Rabon ya ga 'yar gidan Alhaji Salisu ya ce yana so. Bai
kuwa sha wahala ba yarinya ta amince duk da suna sane
da abin da ke faruwa tsakanin iyayensu. Kai tun yara
sun