a kalli Aminu sama da kasa a raine
"Ban gane abin da kake nufi ba. Ina Asama....?"
"Na ce ma ita na zo nema."
"To ai kai zamu tambaya inda take domin ta fice da
daddare an ce kuma ana tsammanin tana wajenka."
Gabansa ne ya fara faduwa kafin fuskarsa ta sauya,
tabbas yanzu ya san Asama'u guduwa ta vi. To amma ina
labbaci?
Fuska a yakune ya dubi maigadi.
"Ban gane abinda kake nufi ba, kana nufin yanzu
Asama'un ba a ganta ba?"
"Ka fini sani." Uba ya ce masa cikin gadara, domin
a tunaninsa Aminu na kokarin raina masa wayo ne bavan
an ce Asamalu tana wajensa. Kume dole ne ya yi hakan
52
tunda an ce sakacinsa ne ya ba Asama'u damar guduwa.
Aminu ya dukar da kai cikin tsananin damuwa.
"Gaskiya Aminu babu dabara ga zaman mu, amma
idan ka ce haka ba komai ni zan tafi."
"Ina za ki?"
"Duk inda ta kama." Ya tuno abin da ya faru
tsakaninsa da Asama'u a daren yau.
Yanzu ya yarda a irin furucin da ya fita daga bakin
Asama'u ba shakka za ta iya guduwa.
"To amma ina zata?" Shi ne abinda yanzu
zuciyarsa ke son sani.
Lallai yana matukar son Asama'u domin yanzu da
yake a tsaye zazzabine ke yunkurin lullubeshi.
Bai damu da hakan ba, yanzu tunaninsa. Ina zai
samu Asama'u?
"Duk inda take sai na nemota, don ba zan iya
rayuwa babu ita ba..." Zuciyarsa ta ambata.
Cikin fushi ya juya ya nufi gida ya bar maigadi
Uba anan.
Jikinsa a sanyaye ya shiga dakinsa kai tsaye ya
nufi gadonsa ba tarc da ya tube takalmansa ba. Ya fada a
kai rub da ciki. Cikin kunar zuciya va ke furta.
"Asama'u ina kika tafi ne? Ya ya kika yi min haka?
Me ya sa ba ki jirani ba? Kina sona kuw...." Tunaninsa va
katse sa'ar da ya tuna lokacin da Asama'u'tá zo ta nemi su
tafi ya ce bai yarda ba.
"Ba laifinki ba ne...ba laifinki ba ne....Asama'n" Ya
shiga furtawa cikin sassanyar murvar nadamaa
53
A hankali ya birkice daga rub da cikin da ya yi
zuwa riginginc. Ya zuba wa silin ido ko kiftawa ba ya yi.
Sannu a hankali sai wani tunani ya darsu a zuciyarsa
tunanin daya fatattaki zargin da ya ke yiwa kan sa da
wanda yake yiwa masoyiyarsa. Tunanin kafiyar
mahaifansu, ba shakka ita ce ta kawo faruwar wannan
guduwa ta Asama'u kuma ba shakka ita ce ke yunkurin
ingiza keyarsa shima ga barin garin.
Ya yi nannauyar ajiyar zuciya, a lokaci guda
fwalla mai dumin gaske, ta soma gangarowa daga cikin
idanunsa tana bi ta kumatunsa izuwa matashin kan da ya
dora kansa a kai.
Lallai yana da bukatar sanin wannan mummunar
gaba ta iyayensu da makasudinta, wadda har take
barazanar kawar da rayuka biyu daga doron kasa.
"Baba me ya hada ka da mahaifin Asama'u." Ya
shiga ambata a fili kamar wanda ke magana da mahaifin
nasa.
Bai samu amsa ba, ba ya kuma tunanin samu,
kuma koda zai samu ma baya bukatar yanzu. Babban abin
da yake bukata a yanzu wanda ya fi damunsa shi ne sanin
inda masoyiyarsa ta tafi.
"Oh! Yanzu ko a wannc hali Asama'u ta ke, dadi
ko wuya, oho?" Zuciyarsa ce ta saka masa. Ta ke sai ya ji
kamar an tsikara masa allura.
Ya yi zumbur ya tashi zaune, kai tsaye ya mike
tsaye, cikin kuzari kamar ba abin da ke damunsa ya nufi
babbar jakarsa da ke dauke da kayansa, ya bude. Ya soma
birkice kayan da yake ciki. Ba wani abu yake nema ba
kudi vake nema.
Ya daukosu sababbi fil da su Ya mayar da jakar ya
54
rufe, sannan ya tashi ya nufi teburin littattafansa ya dauki
makullin motar sa da gaggawa ya yi waje, har ya nufi
dakin mahaifinsa sai ya kuma komawa ya dauki hoton
Asama'u da ke ajiye cikin dubban hotunan dake cikin
album, ya kuma ficewa.
A daidai lokacin ne motar 'yan sanda cike da su ta
ja ta tsaya agaban kofar gidansu Aminu, baro-baro rubuce
a jikin motar,ANTI CRIME.
'Yan sandan suka fara diddirowa hannunsu rike da
bindigogi kamar sa ci babu.
Alhaji Masa'ud dake bin su cikin tashi motar shima
ya bude ya fito.
"Nan ne gidan." Ya ce cikin fushi.
Daya daga cikin 'yan sandan ya isa kofar gidan ya
tsaya, kamar an wurgoshi ya fito.
"Yauwa! shi ne wannan!" Alhaji Masa'ud ya ce a
harzuke yana nuna Aminu da ya fito cikin sauri.
Kamar kura taga kare 'yan sandan suka nufi Aminu
kowanne na gyara zaman bindigar a hannunsa.
dashi.
"Malam you are under arest." Wani sajen ya ce
"Menene ya faru?" Aminu ya bukata a rikice ganin
wani dan baki kakkauran kurtun fan sanda na kokarin
dadumarsa.
"Za ka ci ubanka ne...sai an je can kasan abinda ka
yi munafuki...6arawon mata." Alhaji Masa'ud ya cс а
fusace.
A daidai lokacin ne Alhaji Gambo mahaifin Aminu
ya fito. Dumu-dumu ya ga dansa Aminu a hannun yan
sanda suna jan sa,Alhaji Masa'ud babban makiyinsa na ta
kwarara masa zagi...!
55
Zan ci gaba a na biyu
Ya ya za a yi tsakanin Alhaji Gambo da Alhaji
Masa'ud babban makiyinsa,Alhaji Gambo zai bari a tafi da
dansa kuwa?
A ina Asama'u take,wacce rayuwa ta kasance a ciki
bayan barin ta gida?
Za ta dawo kuwa? Ko za a nemo ta ne? Idan ta
samu waye zai aureta tsakanin masoyinta na hakika Aminu
da dan uwanta Yusif?
Ku biyo 'yar uwarku
Zainab Lawal Brigade
08029460293
Don samun amsar wadannan tambayoyi..