NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 8 of 37

gidan Mallam Isa mijin Yaya Amina, Saminu zaune a kofar gidan bisa dakali kanin Hadiza ne mai bi mata anan gidan Mallam Isa, ya mike da sauri ya nufi su Yusuf domin wani ikon Allah a duniya babu wanda Saminu ya ke gani da girma irin Yusuf. Dalilin kuwa shi yaro ne bai da mantuwa å lokacin da Yusuf zai auri Hadiza a duk lokacin da Yusuf ya zo gaida Yaya Amina, Yusuf ya kan rungume Saminu ajikinsa ya na sai masa biskit yana ba shi labarai tare da nuna mashi muhimmancin ilmi don haka ne Saminu ya mike da neman ilminsa a yanzu har yа shiga jami`a neman zama cikakken likita. To ko da ya ji ance an fasa auren yayarsa Hadiza daYusuf dauka ya yi lokaci ne bai yi ba, ko kuma Hadizan ce ta bata masa rai amma da ya ga aure ya zo tsakanin Hadiza da Amiru sai ya yi murna ga samun miji ga Hadizan to sai kuma mai? A daren jiya sai ya ji Hadiza na gaya ma Gwaggo cewa Yusuf ya dawo da niyyar aurenta, sai ya ji Yaya Amina na masifa kamar ranta zai fita ita ma Hadizan na taya Yaya Aminar masifar shi ne Saminu ya ce`menene na masifa haka amma kun san da Baba Kado na da rai dole ne a maida auren kansa, kuma ma ni banga laifinsa ba wanene a duniya ba ya yin kuskure? Tunda har ya gane kurensa ni ina ganin ai 16 gara na gida wanda aka saba da iyaye da kakanni'. Hadiza ta се "Idan ka isa sai ka zo ka kaini gidan Yusuf koko a yau ka haifi diya ka ba Yusuf karewar kauna daga yau bana son ka kara saka sünan mahaifina cikin al`amuran Yusuf ya na kaunarsa ya ci mana mutunci?" Saminu ya fice ya kyale su. To yanzu da hantsi kwatsam sai ga Yusuf. Saminu ya amshe su hannu bibbiyu ya kai su dakinshi na zaure, Yusuf ya ce, "Saminu an ce Hadiza na nan ko?" Ya ce "tana fa nan". Ya ce, "to don Allah don son manzonSa je ka ce ina son ganinta." Suna zaune a tsakar gida suna gyaran kayan miya Yaya Amina da Hadiza, Saminu ya shiga cike da fara'a ya ce, "Don Allah idan kina son saduwa da rahamar Manzo ki zo ku gaisa da Yusuf". Ta galla mai harara ta ce, "Saminu ni dai ba na wasa da kai kuma ko muna wasa ba na son maganar Yusuf domin ni ba shaidaniya ba ce ka ce ya fita hanya ta ban ga dalilin da zai sa ya matsa man ba". Nan da nan tsiya ta kaure tsakanin Hadiza da Saminu har ana neman a gaya ma juna magana, amma sai yaya Amina ta yi karaf ta ce, "Ni ina ganin har da laifin Halima uwar Yusuf, idan ba har Halima ta zama shashasha ba yaya za ta kyale Yusuf har ya dawo gare mu? To idan yana iko da ita mu ba ya iko da mu mai akai akai Halima balle wani danta Yusuf?" Anan ne kuma Hadiza ta sadda kanta kasa zuciyarta ta rinka bugun uku uku, me zai kai Yaya ta rinka zagin Gwaggo Halima koma menene ai Yusuf yai masu ba ita ba, haka nan kuma ita Yaya ai babbace me zai sa ta zagi Gwaggo Halima, bayan ta tabbata su Yusuf za su iya jin wannan zagin domin dakin Samınu da tsakargida ba wani nisa ne da shi ba a kalla komi Yusuf yai masu iyayensa sun fişkarfin zagi a wajensu kamar yadda ta yi ımani komi zai hada su da Yusuf ba zai taba iya zagin iyayenta ba. Daga Hadiza har Saminu sai suka yi shiru takaicin zagin Yaya Amina kawai ya ishe su, Saminu ya juya ya koma wajen su Yusuf ya na basu hakuri. Babu tantama sun ji zagin Yaya Amina domin Yusuf din cewa ya yi don Allah ka shiga ka ba Yaya Amina hakuri ka ue idan da hali ta ba ni dama na shigo na yi mata bayanin irin yanayin da Gwaggo Halima ta shiga a 17 lokacin da na yi kuskure, amma wallahi Gwaggo ba ta da laihi ni ne mai laihi." Saminu ya san halin mahifiyarsa don haka ya rinka bawa su Yusuf hakuri akan su tafi kawai babu komi, shi kuma Yusuf ya kafe a dole aje a baiwa Yaya hakuri a roki arziki shi ma ya shigo ya wanke Gwaggo Halima. Saminu ya shigo ya na ba Yaya hakuri amma sai ta kara haukacewa tana fadan cewa wannan danyen kai ake son aka wo mata. Hadiza ta ga an kwashi lokaci mai tsawo ana jayayya kan magana daya, ta riga ta san halin Yusuf mutum ne mai kafiya da shegen nacin tsiya idan ya nace kan abu sai ya ga karshensa kafin ya dangana saboda haka kawai sai ta mike ta shuri silifas din ta sai kofar gida. Saminu ya bita yana rada mata "Anti Hadiza kin dai san karshen mai wulakanci, don Allah ki bi sa a hankali ku rabu lafiya ban da wulakanci, mutanen nan komi ya yi mana mahifiyarsa ba ta cancanci zagin da Yaya ke mata ba." Hadiza dai ba ta ce masa uffan ba. Ta isa dakin Saminu ta yane labulen ta shiga ba ta zauna ba, sai kawai ta jingina ta mayas da hannayenta bisa kirjinta ta murde fuskarta ba alamar walwala. Ta yi ma Yusuf kyau fiye da kullum, idon ta sumul ba kwalli amma sai yusuf ya ga kamar mata su daina adon kwalli za su fi kyau a idonsa.Tsayinta ya mike sámbal cikin nan ya dafe daf sai kace kirar kwalbar coca - cola. Yusuf ya tsumu ya yi ajiyar zuciya sannan ya nuna mata kujera da hannu ya ce "To zauna mana Hadiza". Ta dube shi ido cikin ido dubar rashin mutunci ta ce, "Yusuf ba zama nazo yi ba na zo ne don na gargadeka kawai, don Allah ka daina zuwa inda na ke, domin ni babu komi tsakanina da kai." Falank
🏠