ya sanar da ita zuwan Yusuf tana tunanin duk
yadda akai akwai magana cikin Yusuf har ta vi niyyar kiran
Falanke ta tambayeshi amma sai ta yi tunanin wannan rage ma
kanta daraja ne, koma menene idan Yusuf na so ta ji shi zai
sanar da ita.
La'asar ko na yi sai ya Basiru ya iso da sauri ya ce,
"Gwaggo ga Yaya Yusuf ya iso, ga direban shi nan da kaya ya
ce akawo maku sannan a kai masa abincinsa can gidansa.
Bayan Basiru ya gama shiga da tsarabar Yusuf ya ce,
"Yaya Yusuf ya ce manshanu da kifi da suka fi yawa na babban
gidan Mallam Tukur ne danyen kifi kuma na Mallam din ne.
Gwaggo Halima ta ce,. "Au to ku tafi da shi mana idan kun aje
ma Maitama abincinsa ba sai ku je can gidan mallam din ku kai
masu ba? Kwa ce ina gaishe su".
Yusuf bai sami zuwa wajen Gwaggo Halima ba sai bayan
sallar isha'i. Tunda ya iso ya kira Falanke don yaji bayanin Hadiza
bai ji dadin rifot din da Falanke ya kawo mashi ba, amma sai
Falanke ya ce, “Haba Yallabai bana son ka nuna ragwanci ka
tuna ka yi laifi tun farko don haka tunda mun gani muna so dole
mu yi shirin daukar duk wulakancin da za`ai mana mu dai burin
mu idan bukata ta biya ai shi kenan.
Zancen Falanke haka ya ke, to amma matsalar da bai gane
ba ita ce wai ta ina zai shawo kan Dije ta wacce hanyar? Ko
alama maganar janyewa ya san ba tashi ba domin son Dije ya yi
tasiri a zuciyarsa har bai son ya hasala komi in ba al`amuranta
ba. Babban takaicinsa yanzu shine bai so Gwaggo Halima ta ji,
don gudun kada ta hana shi a dalilin Amiru, shi kuma a gaskiya
ya yi niyya babu fashi sannan kuma bai son bata wa Gwaggo
Halima, to yana cikin`yan shawararinsa da zai gaya ma Gwaggo
Halima idan ta kawo mai cikas.
Ya isa gidan ya cimma Gwaggon na kaye-kayen kwanonin
da ta wanke wa'anda aka kai ma Yusuf din abincin dare yace,
"Salamu alaikum Gwaggo ko kun ganni". Ta vi murmushi ta ce,
`mun ganka yanzu da ka shigo'. Ya ce, `ku yi hakuri Gwaggo
14
wallahi jama'a ne wannan ya je wannan ya je kuma kowanne da
matsalar sa dole ne kuma mu saurare su tunda sun haifemu". Ta
ce "ai hakan shi ne mai kyau ai arzikin jama'a shine arziki, shiga
dakin ina zuwa". Ya zauna na dan lokaci ya dauki wani littafi na
tauhidi yana dubawa da ya ji shigowarta ya aje suka gaisa sannan
tabo can tabo nan na hirar da da mahaifi, can daja sama Yusuf
ya rinka matsa yan yatsunsa ya ce, "Yanzu saboda Allah
Gwoggo ashe kun san Hadiza ba ta yi aure ba, amma ba ku taba
yi man maganar ba illa kullum ku matsa man in yi aure?" Ta yi
jigum ta na kallonsa ta ce, "wacce irin magana ce wannan
Maitama? Dijen da ka sa na dinga zúbda hawaye akan ka aureta
ka ki, to don mi daga bay a zan dinga yi maka nacin maganarta?"
Ya ce, "To amma Gwaggo kun san Dije ta canza ba kamar da
ba." Ta yi dariya ta ce "au kai da haka ka ke ai kaima ka canzar"
Ya ce “To ni dai gaskiya Gwaggo in zanyi aure to Hadiza zan
aura". Ta dau lokaci kafin ta amsa tace "Maitama in kayi haka
kuwa ka kyauta kenan? In ce Amiru ake maganar ansa masu
rana yadda naji labari mai an ce, akwatunan lehen sa a kasashen
turai ya hado su wasu sun ce shidda ya yin da vvasu ke cewa
dozin ne.
Yusuf ya sha mur ya ce, "Ni Gwaggo ina ruwa na da
wannan, ni har ga Allah da zuciya daya na ke son Hadiza don
haka ba na jin zan iya bar ma Amiru sai dai in Allah ne bai ba ni
ba."
Itama Halima ta shiiga tunani to yanzu akan Amiru za ta ki
na ta ne? Balle ma yadda ta zaku da ya yi aure, sai dai tana ganin
wata babbar matsala ce domin ta san Hadiza da wuya a shawo
kanta idan an tuna da, illa dai kawai ta na ganin wannan ita ce
damar da ya dace ace danta Yusuf yai aure haka nan, balle samun
mace kamar Hadiza ba karamin shiryuwa ba ce a gidan dan ta Yusufa.
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, "za mu ta ya ku addu'a akan
Allah ya zaba abinda yafi alhairi. Idan aure da kai shi ya fi alhairi
Allah ya mayas kanka, idan kuma da Amirun shi ya fi alhairi. Allah ya kara kullawa."
Yusuf ya yi murna da amincewar gwaggo sai ya ji wani karfi tamkar ya shawo kan Hadiza.
15
Wanshekare da safe ya sha ado da wata tsaleliyar shadda
dogon wando da riga, ta yi mai kyau dan birni dan boko sosai
yana janye da motar Falanke na zaune gefensa, sun nufi gidan
Inna Tambai wajen Hadiza, sai Falanke ya ce, "Yallabai albishir a
gareka". Yusuf ya ce, "mai kuma ya faru?" Falanke ya ce, "wai naji ance an mayas da bikin Hadiza sai ranar da za` ai sadakar
arba'in din Baba Kado". Yusuf ya yi murmushi har kwarjininsa ya
bayyana ga lafiya na tumbatsa kamar ruwan da ke sauka daga
samaniya.
a
Ya fito daga cikin motar ya jingina daga gefen motar ya
tsurawa wa zauren Inna Tambai ido ya na jiran ya ga fitowar
Falanke tare da Hadiza, amma sai Falanke ya fito fuskarsa
yamutse ya ce, "Yallabai wai kuma kaji wai Hadizanna
Malumfashi?" A cikin rudewa ya ce, "yaushe ka ji ana cewa za
ta dawo?" Falanke ya ce, "ni ban gane kan Inna Tambai ba na
yi ma ta wannan tambayar ta ki man hannu". Yusuf ya sadda kai
ya yi shiru ya ce shigo motar mu je Malumfashin. Suna isa
Malumfashi