NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 6 of 37

ke ya yi masu sallama ya tafi da niyyar sai ya dawo gobe saboda jin bayanin amsar wasikar. A can Abuja kuma Yusuf sai ya ga ai lokaci na kara kurewa mai zai hana ya bi Falanke gobe jumma'a don ya kara yin dan kokarinsa a kan Hadiza? Saboda haka sai ya yi ma kanensa Basiru waya wanda ke aiki a konannen bulo da ke Funtuwa, cewa idan ya koma Bakori ya sanar da Falanke kada ya taho gobe va jira shi zuwa ga shi nan tafe gobe jumma'a. Hadiza ta yi tagumi tana kallon rubutun Yusuf wanda shi ne ya ki ta anan gidan Inna Tambai kuma yau shine mai wannan wasikar cike da kalamai a dakin duk a dakin dai Inna Tambai wanda ita a ganinta wannan wasikar ba komai ba ce bayan bala'i ga wasıkar Sallama a gareki Dijena, 11 Sallama a gareki Dijena, Bayan miliyoyin addu`o`en da na ke mikawa wajen Sarki Allah akan ya yi ma BabaKado rahama da gidan aljanna, ya Allah ya ragwantawa Baba kado halinsa na alhairi ya sa ya bisa amin. Mu kuma da muka rage ya bamu guzirin cimma sa amin. Hadiza don Allah don Annabi ki bani aron kwakwalwarki ki tsaya ki yi tunani sannan ki auna maganganun da zan gaya maki. Da farko dai ina son kisani a duk lokacin da Allah Subahanahu WaTa'ala zai yi hukuncin baiwarsa akan wasu adilan bayinsa guda biyu wato macen kwarai da namijn kwarai ya kan jarabancesu ta hanyoyi da dama haka nan za ki ga ya'yan ya ku bayi wa'anda ba su aje ba basu ba wani ajiya ba Ubangiji ya yi masu kyautar 'ya'ya masu kyau da kwarjini da basira wa'anda akarshe sai kinga 'ya'yan nan sun cilla duniya ko'ina an san da su bayan iyayensu ba kowan kowa bane. To anan na san babu ko shakka ni na san wata baiwar Allah ce haka nan kema wata babbar baiwa ce a duniya, ina kuma tabbatas ma ki abinda ya gudana a tsakanina da ke ba komi ba ne face jarabawar Ubangiji. A lokacin da aka so aure na da ke Allah ya yi nufin abubuwa da dama akan ki na samun daukakar duniya da lahira wanda ta yiwu a lokacin in da mun yi aure, matsalolin aure su tauyeki har su hana ki kai matsayin wayewar da ki ke a yanzu. Ni kaina ko da na yi aure kila rabo zai kai ni amma daukaka ta da darajata suna wajenki dole Ubangiji ya sake kawo hanyar saduwarmu har mu yi aure sannan na cimma sauran alhairina. Lalle na san Baba Kado shi ne usilin soyayyarniu da ke, amma ina son na tabbatas ma ki, Allan ne ya kulla sovayarmu can cikin jininmu don haka ina son ki ba ni dama na nuna maki hakan, domin a yau babu Baba Kado a duniya kuma ga shi ina ji a jikina da gangar jikina alkawarin Allah zai cika akan Yusuf da Hadiza. Hadiza dan Allah ki yi nazarin yadda mu ka rinka shirya rayiwarmu, amma kash! Allah ya hana, to ni abinda na dauki wanna jarabawar Ubangiji ce, saboda ga shi ni yanzu Allah ya kai ni wani matsayin da zan iya rike mace hudu amma bani da 12 ko daya a dalilin rashin ke Hadiza wadda aka halitta Yusuf dan ita, yayin da ke dinma na san dole ki sha kwaranniya da yan maza a bisa baiwar daraja uku da Allah ya yi maki wato kyau na usuli, ilnni da samun iyaye dattawa amma kuma mijin bai bayyana ba wato ni kenan da aka halittaki domin ni. Hadiza don, Allah kada ki tauye mana hakkinmu, ki yi hakuri ki gafarce ni a bisa kuskuren da na yi ma ki a can bay a, ki yafe min ki bar ni na fito mu yi aure, wannan ranar da aka sa ma ki ban a son a canza sai dai a maido kai na. Hadiza ki tuna babu wanda bai kuskure a duniya, na tuba ki gafarce ni, Insha Allah ba za ki taba samu na da saba mа ki ba, domin ina son ki son da ban taba zaton zan yi ma dan Adar Kacda ki ce, tafi can mayaudarin banza wallahi wallahi Hádiza ke kadai na ke so, wancan son da na yi ma Fa'iza son kuriova ne amma son ki na gaskiya ne domin na so ki da kuniciya yanzu kuma ina sonki a lokatin da na mallaki hankalina. Bana tsammanin zan iya son wata mace kamar ke, don haka a da Baba Kad'o ya hadamu amma yanzu mu za mu hada kan mu, Insha Allah wannan soyayyar ta mu sai ta kai ma Baba Kado har cikin Aljanna Fiddausi. Na ki mijinki Insha Allah Yusuf. Hadiza tasa hanmu ta goge kan hancinta, duk kalma daya da Yusıf ya rubuto ta razana ta sai dai har yanzu zuciyarta ibata saduda ba, tana ganin babu abinda zai raba ta da Amiru, ko wacce irin daukaka Yusuf ke hango masuita kam tafi ganin ta wajen Amiru illah dai kawai daga ita har Inna Tamban kalaman Yusuf sun razana su, Inna Tambai ta ce, "ke kin ga min yaro in da duk ya kashe min jiki da daddadan maganganu? Tamkar an yo masa wahayin maganganun?" Hadiza ta ce, "Rabu da shi kawai Inna, shedananci ne rin na sa, wa ki ka taba ganin an yi wa wahayi in ba Annabin rahama ba? Wallahi idan kana sauraron irin su Yusuf sai su halakar da mutun." Inna ta yi ajiyar zuciya ta ce, "Gaskiya ne maganar ki ai wannan sai mu rinká neman tsari da shi kar ya ja mana fitina cikin gari. Hadiza ta, yi murmushi ta ce, "Nan fa ya yi karya Inna 13 Insha Allah, tunda ya kawo kan shi gare ni, to sai ya raina kan shi, sai na nuna mai iyakar sa a garin nan." Washegari Gwaggo Halima ta fara shirye-shiryen abin ci domin Basiru
🏠