NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 5 of 37

wannan rasuwa da ta gitta, a jiya ni da Mallan Hiya da Hadiza mun sake shawara akan ranar bikinku an daga mun mayas ranar da za'a yi arba'in din marigayi Alhaji saboda, ka san bikin ba zai yi armashi ba daga rasuwa a kama shagalin biki." Amiru ya ji zuciyarsa ta buga dam, babu halin ya nuna wata alamar cewa ya damu, domin nuna damuwarsa tamkar nuna bai damu da bacin ran Hadiza ba kenan na game da rasuwar mahaifinta ya ce, "Allah dai ya jikan Baba", aka ce "Amin" Ya kwashi Hadiza da Inna Tambai da kayansu ya kai su gidan Inna Tambai, ta yo mai rakiya har cikin mota tana kara yi mai godiya a bisa dawainiyar da ya yi masu tun daga asibiti har zuwa yau, ya ce, "Babu komi yanzu ran lahadi za ki koma Kaduna?" Ta ce` Insha Allah' ya ce "Zan yo waya da yamma kenan." Ta koma dakinlinna Tambai nan da nan ta dora ruwa bisa wuta don ta yi wanka, domin kwana bakwai din nan jin jikinta ta ke yana yi mata danko, ta lalubo wani akwatinta cikin wa'anda ta dawo da shi daga Hajji anan kalkashin gadon Inna tambai ta duba man shafawarta wato zaitun domin shi ne man Hadiza, rudanin ciwon Baba Kado bata tsaya ta dauko ba sai dai ta dauko sabulun wankanta wato sabulun salo amma dan Ghana wanda tàke cakudewa da zuma yar usili da jar kanwa da kwai, idan ta yl wanka da wannan sabulun sai ta mulke jikinta har gashin kan ta da man zaitun wannan shi ne sirrin Hadiza na ko yaushe fatar 9 jikinta na salki da sulbi, haka nan idan mata sun kai dubu launin fatar Hadiza ta fita daban tamkar danyar roba ga sheki da salki. Da la'asar şakaliya suna zaune ita da Inna Tambai suna maimaita ciwon Baba Kado wani yaro ya shigo ya ce, "wai a zaure ana sallama da Hadiza!" Kamar ta ce `Ace ya shigo' ta san`yan gaisuwa amma sai ta dauki mayafinta ta nufi zaure. Ta sami Falanke tsugunne a zaure ta ce, "A'a Shu'aibu telan zamani? "Barka da fitowa ranki shi dade ya karin hakurin mu?" Ta ce "mun gode Allah". Anan fa Falanke ya shiga yabon Baba Kado ya na nuna wannan rasuwa ta jama'ar Bakori ce gaba daya inda yake shiga ba ta nan yake bulla ba, a bisa kyakkyawar lafazin sai Hadiza ta ji wani sanyi a ranta ta rinka raya ma ranta cewa mahaifinta na can Aljanna Fiddausi domin yabon jama'a shi ne rahamar mamaci, ya ci gaba da cewa "yanzu duk dattawan garin nan akwai mai halin dattako irin na Baba Kado? Ki duba fa saboda dattakonsa yaron nan Yusuf ba shi da komai amma Baba ya ce ya ba shi ke sai dai kuma wani shaidan da ya gilma Allah bai ida nufi ba lokacin, amma mu masoyan Baba Kado muna nan muna rokon Allah yasa ke Hajiya Hadiza da Yusuf sai kun yi aure don a kulla wannan zumunta da marigayi ya so kullawa saboda duk wanda ya san Yusuf ya san ya zama abin tausayi saboda ga dai dukiyar ya tara amma ya kasa auren a dalilin tunanin abinda ya yi ma ki Hadiza da Baba" anan sai Falanke ya sa habar riga ya rinka goge kwalla, "takaicinsa a kullum bai da inda zai samu labarinki sai a wannan mutuwar Allah ya hada shi da ke." Hadiza ta tsargu da abinda Falanke ke nufi babu tantama wasu zancen banza ya ke nufi don haka ya tsuge da magana ta juya ba tare da ko sai anjima ba ta shige gida. Anan fa Falanke ya yi turus kai wannan shawo kanta sai Allah, tunda wa'annan maganganu ba su ratsa ta ba bai san kuma irin wanda zai yi mata ba. Ta zauna kusa da Inna Tambai tana ta fada tana fada mata abinda Falanke ya zo da shi. Inna ta ce, "kai anya Yusuf zai aiko shi da irin wa`annan maganganun?" Hadiza ta ce "wallahi Inna zai iya ban fa gaya maku ba ne kin ga rannan sai da ya fara min wasu maganganuan na kyale shi na shige gida abina, shi kan shi 10 Amiru na lura yana zargin Yusuf da abubuwa da dama sai dai kawai yana dannewa ne saboda mutuwar Baba". Anan Falanke ya kara aiko wani yaro`wai Shuaibu Tela ya ce wai Hadiza tai mai arziki don Allah ta zo!' Hadiza ta ce, "kai fita ka ba mutane waje ka ce na ce ya fita hanya ta". Sai Inna ta ceba haka za'a yi ba, je ka ce na ce ya shigo cikin gidan.' Inna ta mike ta fiddo tabarma ta shimfida masa daga can nesa, yayin da ita Hadiza suke zaune a bisa wata tabarmar a bakin kofar daki. Haba sai murna wajen Falanke aka shiga gaisawa da Inna Tambaya, sannan ya ci gaba da yabon Alhaji Kado kamar yadda ya yi ma Hadiza a zaure kowacce ta yi tsit ta na sauraronsa sai ya kutso maganar Yusuf kamar yadda ya fara. Inna ta ce, "kai Shuaibu kar ku mai da mu mutanen banza in dai batun Hadiza ku ke yi ba mai samu mu ji kunya a kasar nan, don rasin kunya zai ce bai san inda zai samu labarin Hadiza ina ce ya na zuwa gaida marigayin? Kuma ai ni ba bakuwarsa ba ce bai zuwa ya tambayan, to tsaya na gaya maku ba na son na kara jin zancen Hadiza a bakinsa, auren su ita da Amiru ba mai fasawa". Falanke ya ce, "kin san Allah Innarmu tsoro da zullumi da jin nauyi ya hana Yusuf zuwa gareku don ya ji labarin inda Hadiza ta ke, ya gwammace yai ta zama a haka cikin jimame da damuwa a nan ne ya fidda wasikar Yusuf ya je har gaban Hadiza ya aje, bata taba ba haka nan bata tsinka masa ba. Ya mi
🏠