NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 4 of 37

wallahi ban taba jin wadda na ke so ba, har na yi sha`awar aurenta a zuciyata. Sai dai matsalar yanzu itace Falanke wannan Dijen da na ke maka magana ita ce Hadizan da Amiru babban aminina zai aura, diyar Baba Kado." Falanke ya sa hannu ya toshe bakinsa ya yi shiru yana mai girgiza kansa sannan zuciyarsa cike da al`ajabi, shi kan shi yana mamakin Dijen da ya sani wadda ke tallar goro itace wannan ta zama sai ka wanke hannu ka taba ta. Ya dubi Yusuf ya ce, "Yanzu Dijenka ce ta koma haka Yallabai?" Yusuf ya yi murmushi ya ce, "Wallahi ita ce, Falanke". 6 Falanke ya gyara zama ya ce, "To ai Yallabai sai an gwada akan san na kwarai, kuma ma ai mata tafi amini, ba wai zan hada ka da Amiru ba ne, amma gaskiya duk hanyar da za mu bi ya dace mu bi ta ka amso matarka". Yusuf ya yi ajiyar zuciya ransa yayi kal tunda ya sami goyon baya akan aurensa da Dije. Ya ce, "E Falanke to yanzu yaya ka ga zan bi na shawo kan Dije, ka san dai ba karamin tashin hankali ba ne, raba ta da Amiru da kuma kuskuren da na yi mata tun farkon rabuwarmu, maganar dai na rude ta da kudi wannan shirme ne, domin me za` a nuna mata yanzu, ko shi Amiru ya yi kadan ta aure shi don kudinsa ballantana ni, wanda na ke takama shi ne Baba Kado ya rasu". Falanke ya ce, "Wannan duk haka ne, abinda za`a yi shi ne ka shirya takarda ka rubuta ban hakuri duk wanda ka ke iyawa, ni kuma zan je ran jumma` a na kai mata tunda shi Amiru ran alhamis zai bar Bakori idan na dawo ran asabat muna iya komawa ran lahadi, ko ya ka gani?" Yusuf ya ce, "A`a ran alhamis za ka tafi, jumma` a zai ka zo na ji yadda ku ka yi, domin na san ran alhamis da wuri zai bar Bakori saboda haka na san ba za ku hadu ba." Aka bar ta a haka ya koma falo ya cimma Suzi na nan na jiransa, ya rungumeta suka nufi dakin baccinsa, sannan ne Suzi ta yi ajiyar zuciya. Yusuf ya fara aiki da kwarjini de daukaka sannan da iya aikin, har ya kai kaf a kamfanin kamar shi ne Babba saboda kwarjininsa da tsare aikin kuma babu hainci a bisa aikinsa а dalilin hakan shuwagabanninsa ba su jin kyashin sakar masa dukiya don suna ganin ya cancanci hakan saboda kwazon da ya ke nunawa kanfanin. Yusuf kafin ya ankara ya zama daya daga cikin sabbin matasa masu tashen kudi a birnin tarayya Abuja, to` yan mata kuma da suka kyalla suka hango motar zamani ga saurayi matashi mai cikan halitta a ciki, sannan namiji daya da daya a 7 cikin maza, mai tsarin kyau na usili, ga cikar lafiya, tamkar don shi kadai a ka shirya rayiwa a kullum cikin shi shar kamar jariri sabon haihuwa, abinda ma ya fi birge mata akan Yusuf shine kwarjininsa ai fa shi kenan ko bai je ba a zo masa, wannan ya kara dasa tsanar mata a zuiciyan Yusuf va rinka ganin kamar duk mata halinsu daya, ya zame masa canza mace kamar yadda zai canza takalmin kafarsa. A kullun aiken Gwaggo Halima ya zo ya yi aure amma shi yana ganin auren ba dole ba ne tunda ga matan nan yana biyan bukatarsa da su, da wuya Yusuf ya yi nema da hausawa sai dai wasu kabilu daban. Yusuf kenan. Amiru fa? Jirgi daya ya debo su da Yusuf a kullum fadan da iyayensa ke yi kenan akan lokaci ya yi da zai aje mace, domin duk kannansa sun yi aure sun hayayyafa amma shi ya ki. To mararrabar Yusuf da Amiru daya ce: Yusuf `yan mata ya ke nema yayin da Amiru shi kam sai matan aure, ko mi mutuncin auren mace muddin Amiru ya kyalla ido akan ki yana so sai va yi yadda ya nemi ki, da zarar kun yi nisa da nema zai ma ki alkawarin aure to da kin kashe aurenki shikenan kin zame wà Amiru jidali zai fara gudunki sai kuma a shiga rayuwar wani gidan (Allah ya shirye mu, amin) Wa'annan samari biyu`yan fitina su ke son diyan Baba Kado da aure, (kamilallah Hadiza). KASHI NA GOMA SHA UKU Ranar alhamis da sassafe a ka taru a kofar gidan marigayi Alhaji Kado akayi masa addu`a, a cikin gida ma haka, sannan ga abinci nan kala-kala an dafa a ka rinka bayas wa sadaka. Misalin karfe goma na safe Amiru ya shiga har dakin da su Hadiza su ke, ya same ta ita da Inna Tambai da su Ankudi ya ce, "To Hadiza Allah shi kara mana hakuri Allah ya jikan Baba" Aka amsa gaba daya "Amin Amiru Allah ya saka maka da alheri kuma Allah ya ba ku`ya`yan da zasu jikanku haka." Amiru kan shi a sunkuye hannunsa na bisa yatsansa na 8 kafa ya ce. 'Amin, to zan koma Kano a yau ina fata babu komi?" Hadiza ta dago kai ta ce, "Ina son ka aje mu gidan Inna Tambai zan kwana biyu can kafin na shige Kaduna, saboda a gaskiya bana iya ci gaba da zama anan dakin Baba, sai in ta ganin kamar zan gan,shi". Su Ankudi a ka yi narai - narai da ido suka ce, "Haba Dije bayan kin gina mana gida muna ta jin dadi kina debe mana kewa kamar Alhaji na nan, kuma za ki bar mu?" Hadiza ta ce "A'a Gwoggo kada ku damu zan rinka zuwa". Inna Tambai ta ce, "Kun ji shirmen naku ko, me Hadizan zata zauna ta yi maku, wadda zata gidan mijin ta kwanan nan?" Amiru ya kara jin sa` ida cikin ransa ya dan muskuta ya gyara zama, amma kuma sai Inna ta ce,Af, Amiru daman akwai sakon da zan gaya ma, a dalilin
🏠