ya ta yara shi ke damunta
wannan hushi da suke yi bata iya baccin kirki, a kullun ji take
kamar ta je dakinsa ta bashi hakuri amma na ta girmen kan da ganin laihinsa sai ta ji bata iyawa, lokutta da dama ta kan sami dalilin da ya dace ace sun yi magana domin hushin ya shige sai girman kai da miskilanci ya hana ta. Ko waya aka yo Yusuf ya kan ki dauka da gangan wai ko Kubra ta dauka tace wayanka
ce, shi kenan sun shiriya amma sai ta ki.
Akwai lokacin da aka yo ma Yusuf waya yana fale yayin da ta dauka a kicin amma don tsabar miskilanci ta:sige shi
kwance a falo ta je har dakin baccin yara ta tayar da Sa adiya
cikin magagin bacci har Sa'adiya na faduwa tace, je ki falo ki ce
ma Dady ya dauki waya. Wannan al'amari ya batawa Yusuf rai
amma tunda yana neman shiri dole ya kyale Kubra.
A ranar da suka wayi garin kwana uku ana wannan
badakar hushi, Yusuf ya kai iyakar galabaita ya kwadaita ainun
da Kubra, komi ya tsaya,mai cak sai sha'awarta kadai, inda duk
yake ya kan zauna shiru, yana neman hanyar da zai-yi magana
da Kubra, domin shi ma mutun ne mai shegan jin kan tsiya.
Yana ofis aka bada sanarwar akwai mitin na shuwagabanni
da karfe hudu na yamma. Yusuf ya koma gida kafin lokacin, ya
cimma Hadiza kwance da wani litafi wai Allura Cikin Ruwa kusan
kullun cikin karatu take shiyasa ta manta da bacin ran Yusuf.
Ya yi kokari ya tanka mata ya kasa amma sai ya samo
dabara ya rubuta mata wasika kamar haka, My Kubra,
Za mu shiga mitin karfe hudu na yamma, amma a yanzu
zan kwanta na yi bacci, don haka ki tashe ni karfe uku dai dai
don kada na makara.
Di Yusuf
Ya je ya aje mata bisa tebir inda ya san dole ta je wajen ta
gani ya yi baccin sama-sama yana son ganin shigowar Kubra don
ya ruke ta. Yana aje takarda ta duba ta yi murmushi, karfe uku
ta murda kofardakinsa a hankali itama ta aje mai wasika a tebirin
da ke gefrn gadonsa ta fice, Yusuf idonsa a kanne yana kallonta,
87
ya mika hannu ya dauki takarda ya ga amsarta:-
Karfe uku ta yi ka tashi kada ka makara.
Kubra.
Ransa ya baci ya mike a cikin hushi ya same ta, rike da
takardar yace, "Me ye wannan?" Ta dube shi tace, "me zan maka,
wanda ya fi amsa?" Ya zura mata ido na tsawon lokaci sai kawai
ya kankameta yace, "Kubra kada fa na mutu! Wallahi kwana
ukun nan na galabaita, zancen yara na gane kuskurena tabbas
ba irin tarbiyar da akai mana ba kenan, na amince zan ba ki
goyon baya amma don Allah a dai na duka ---." Ta sunne kai
bisa kirjinsa tace, 'Di wai ni za kai ma gorin bana sonka bayan a
gabanka uwata ta tsine min saboda kai, duk da haka ban fasa
aurenka shine ---."Ya kammala bakinta cikin nashi yace, "Nace
fa ki yi hakuri ni ne da kuskure na dauki wannan laihin." Ya lalubi
cingam din da ke bakinta ya mayas a bakinsa yana tauna, ya
janye daga gareta yana murmushi, yace, "yau kin biya ni cimgam
dina dana taba baki ada, idan kin tuna na taba ce ma ki wanda
za ki bani sai kin tauna! Kin ga a yau mun zama gamgam."
88
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels i