NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 35 of 37

sa, ga 'ya'ya kuma tubarkallah." Yusuf ya jawo waya ya danna gida, Larba ce ta dauka yace, "ke ina antin taku kira ta?" Kubra ta amshi waya ta се, "Salamu alaikum D ya aiki?" Yace, "An gode Allah". "Kubra yau ina da baban bako sai ki shiriya mana abinci da shi." Tace, "An gama Yallabai." Bayan an tashi aiki Awal da Yusuf suka nufi gida, Yusuf yace "ina fatan za ka kwana biyu a gidana tunda aiki ka zo." Awal yace, "Nagode ka ga na huta sauka a hotel." "Salamu alaikum, I am home Kubra" Nan da nan sa Abdul suka tsinko a guje suna ihu "Oyoyo Dady" Di ya suresu gaba daya. Daga can kicin Hadiza ta bullo a bayanta Larba ce da kayan abinci ta fara shirya tebir. Kubra ta zauna suna gaisawa da Awal, Awal na mamakin yadda Yusuí ya ari mace mai kyau haka fiye da Faiza, ga natsuwa da hankali, kai wasu dai da sa'a su ke a duniya. Yusuf ya mallaki komi na duniya anan ne, Yusuf yaa dariya yace, "Kubra wannan shi ne Awal wanda ya kai ni wajen Faiza ya raba ni da ke." Hadiza ta yi wal tace, "Kai D wacce irin magana ce wannan!" 84 Awal ya yi kasake, kunya da kakabi syka mamaye shi, sai kai anya wannan ce Hadizan shi? Kuma ya kira ta Kubra, ya dago kai ya dubi Hadiza yace, "ke malama za ki iya yadda da hakan?" Tace, "ka dai san halinsa mutun ne mai son tsokanan rigima." Aka kyalkyale da dariya sannan Yusuf ya sa Hadiza ta yi ma Awal gaisuwa. Bayan ta shiga daki ne sun fara cin abinci Yusuf ya bayyana masa lalle Kubra itace Dijensa wadda ya bar ta domin Faiza a hankali ya warware masa labari kaf. Cikin kwana biyu da Awal yayi tare da su Yusuf ya yaba kwarai da iyalen Yusuf har Yusuf yace yana so a baiwa Larba gurbin karatu a Kaduna Poly. Awal ya yi murmushi yace, "Idan Larba ba zata ce min tsoho ba da nace ni har a gidana ma da na ba ta gurbi." Yusuf yace wannan zance na Larba ne, "Abdul kira mana anti Larba." Cikin wata daya rak an kammala da komi Larba ta sami miji ga kuma karatu ta fara. Zaman Yusuf da Hadiza zama ne wanda kowácce mace ke kwandayin samu, sai dai an ce babu dan adam din da kan rasa matsala, to ita kam Hadiza matsalar ta daya da Yusuf wato yadda ya ke sangarta 'ya'yansu, ko ita bata isa a kwaba masu ba, Yanzu nan ya hau ta da fata kuma a gaban yaran, saboda haka kwata-kwata yaran ba su tsoran ta, wani abun haushi abin mamaki shi ne Sa'adiya ce ke tsalle daga saman bene zuwa kasa sai Hadiza tace "Haba Sa'adiya ki fa bari kada ki ji ciwo." Sai ko Sa'adiya ta yi dariya tace, "Ai ko na ji ciwo ke Dady zai ma fada." Abun ya daure ma Hadiza kai idan ta nemi ta nuna ma Yusuf kada su girma babu tarbiya sai yace, 'Haba Kubra, gida nawa su ke yara ne fa!' Me zai faru? Kubra na kicin na shirya ma Yusuf hadadden abincin rana, yara na wasa daga waje, yaronsu mai wanki na shanya ya gama wanki, Sa'adiya na hayewa bisa waya sai Ima yace, "Sa`adiya ki bari fa za ki ji ciwo ke fa ba kya ji." Sa'adiya tace, "Ina ruwa na da kai, banza kawai" karaf a kunnen Hadiza 85 yayin da Abdul ya rugo yana kara gaya mata. Zuciya ta kulle Hadiza ta kama Sa'adiya tana bugunta, har da fitsari domin ba'a taba yi mata irin wannan dukan ba, hatta shi ma Abdul ya tsorata. Yusuf ya cimma Sa'adiya taci kuka har fuska ta kumbura, ya ji abinda ya faru haba ya shiga yarfa ruwan bala'i, yace, "wannan kina son kashe min diya ne ba komi ba, ina abun duka, to wallahi ba zan yadda ba, don ba ki so na sai ki huce kan `ya`yana kada ki manta ina sane da kalaman rashin kaunar da ki ka sha fada min ----'Hadiza ta shige dakin baccinta ta balle babin kuka wannan itace rana ta farko da rigima ta kunno kai tsakaninta da Yusuf. Kowanne ya shiga hushi da juna abinda ba su taba yi ba. A wannan rana Hadiza ta raba dakin bacci da Yusuf, shi ma ya nuna hakan ta yi mai dai dai domin zuciyansa na tafarfasa da kunar zafi akan abinda ta yi ma Sa'adiya. Kwana daya da yini daya suna ta rafka hushi da juna, babu inda su ke haduwa, kafin ya iso ta kammala mai komi na abinci. Idan waya akai mai ko yana falo sai ta hau sama ta kira Abdul ya sanar da shi. A kwana na biyu kai kace gidan an yi mutuwa ne hatta yaran sun rage walwala domin ada sun saba jin dariyar iyayen na cika gida. A ofis yawancin wa'anda suka saba harka da Yusuf sun ga canji amma abinda suka dauka kila wani daga cikin iyalansa ne babu lafiya, ya kan zubawa hoton Kubra ido a ofis tunaninta da sha'awarta su kan dame shi, wai me yasa ta doki Sa'adiya har ta ja sanadiyar hushinsu? Yana jin griman kai akan shi ya fara yi mata magana, yayin da matukar kaunarta da sha'awar ta suka dame shi a zuci, ya rasa dabarar da zai bullo da ita, sai ya lalubi waya ya kirata amma yana jin taushin muryata sai kuma ya rasa abun cewa ya tsinke layin. Hatta jinin jikinsa da fatarsa da hannayensa sun san sun yi wani rashi na 'yan kwanaki. Ko da Hadiza ta dauki waya ba a yi magana ba aka aje ran ta ya so ya raya mata kila Yusuf ne, amma jin zafin abinda ya yi mata ta kawad da tunanin. Tana son Yusuf tana sha'awansa, 86 amma ita kam wannan rashin tarbi
🏠