NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 32 of 37

a sanar da shi bukatar Yusuf, Mallam yace "ban yadda ba, abu duk taron mata?" Nan da nan Yusuf va rude yace, "Baba wai saboda asibiti kuma ga 76 Falanke." Mallam Tukur yace, "Wani abu ne Falanke? Me zai iya yi, haihuwar farko ce fa, sam ka maido mana ita nan Bakori a gabanmu, kai ko ka tafi wajen aikinka." Yusuf ya yi jagwale yana son ya hada ido da Hadiza amma ta ki yadda. Yadda Mallam yace hakan aka yi domin baya da ubar da ya fishi, yace, "Ni abin da yafi damuna shi fa Baba saboda wankan ganye ya ke son a maido ki Bakori ni ko ba don sun yi min ta karfin tisya ba ban yi niyyar su yi ma ki wankan gargajiyar nan ba." Hadiza ta yi dariya tace, "kai D wallahi ka daina irin wannan rudewan akan al` amurana, kada ace ka faye zakewa akan mace, menene idan ma na yi wankan, ina ce suma su Gwoggon sun yi ga su nan sumul ina ma laifinisu, ita Yaya ko kallo cikin ma ya ishe ta?" Yusuf ya shafa kai yace, "Ai itama Yayan da dalili take yi mana haka babu komi mu ci gaba da addu'a insha Allah sai ta yi ma wannan jaririn rawa tana juya shi." Hadiza dai ta rubuta takardar aje aiki ta kuma kai masu kayansu, yanzu ta mike kafa a gidan Yusuf. Ana sauran kwana biyu tafiyar su Yusuf ya hada kayan Hadiza da jariri ya tayas da motar ofis zuwa Bakori sannan wanshekare shi da ita suka isa Bakorin. "Insha Allah Kubra sai na dawo a gabana za ki haifu." Tace, "Haba don Allah D ka yì min addu ar na haihu cikin satin nan mana, don ba ka ji yadda wahalad daukar ciki take ba ni." Yace, "kada dai ki shagale da zarar kin haihu ki ma jaririn addu` o en da na koya maki sannan ki yi kokari ki ba wa ko nas din ce kyamara a dauke ku hoto ke da bebin." Hadiza tace, 'In Allah Ya yarda zon gabatar da komi in dai na haihu lafiya!" Bayan Yusuf ya koma Abuja Hadiza na zaure gidansu na Bakori a nan Inna Tambai ta baro gidanta ta komo gidan su Hadiza yayin da Gwoggo Halima to mayas da gidan waen hirarta, duk dai ana tarairayar Hadiza. Lokacin da Yusuf ya sami kwana tara a London da azuhur Inna Tambai da Hadiza na zaune a falo sai kawai Inna taga Hadiza na fisge-fisge kamar wadda lantarki ke fisga, dan lokaci kadan ta fara canza kamanninta nan da nan Inna ta aiki yaro aka 77 kira Gwoggo Halima da Mallam Tukur. Duk wani kokari na Mallam Tukur amma ina! Abun yace tura, nan da nan aka nufi asibitin Funtua da ita, sun isa tana a some. Kwana da yini babu tabbacin za'a sami Hadiza a raye, a rannan ne Basiru ya yi ma Falanke waya ya zo. Likita ya bada shawara cewa ayi ma Hadiza tiyata shi ne abu mafi sauki a same ta kila. Falanke ya janye Mallm Tukur yace idan dai tiyata za'ai mata yana bada shawara aje asibitin Mayfair da ke Zariya. Kowa ya amince aka nufi asibitin Zariya. Ankudi ce ta nufi Malunfashi cikin mumunnan yanayi tana kuka tana shaidawa Yaya Amina halin da Hadiza ke ciki, Yaya Amina ta yi shiru kamar maganar bata dame ta ba, amma sai ta mike ta nufi kewaye ta rinka tsuga zawo, to yo alwala ta zo ta gabatar da nafila ta roki gafaran Ubangiji ta rinka rokon Allah Ya ba wa Hadiza lafiya, idan kuma ajali ta dauka Allah ya yi mata sakamako da gidan aljanna. Ta yi sallama ta mike tace ma Ankudi "Yanzu su Tambayan suna can asibitin?" Ankudi tana 'share hawaye tace, 'E tunda safe can na baro su, kai Dije kam na cikin hali Ubangiji Ya tayas da kafadar wannan yarinya idan aka rasa Dije mu ai tamu ta same mu, yarinya ita da mijinta sun kama kannansu sun rungume?" Amina ta shirya suka nufi asibitin Funtua itá da Ankudi, suna isa suka ci karo da Sabura tana kuka tace, 'Ai Dije kuma sai yadda Allah Ya yi domin an nufi Zariya da ita za a yi mata tiyata.'Amina ta dafa sandar baranda sai hawaye shar, su Ankudi na bata hakuri, tace idan har ban sami Dije da ranta ba, su Ankudi ku ne shaida na yafe wa Hadiza, Allah Ya yi mata albarka, Allah Ya sada ta da rahamarsa.' Amina da Ankudi da Sabura har bayan la'asar suna jele a garin Zariya kafin Allah Ya ba su sa'a su gano asibitin May Fair Clinic. Sun samu har an yi ma Hadiza aiki. Amina bata kara saduda ba ta kara tsinkewa da raunana sai da ta ga yaddə Allah Ya mayas da Hadiza. Wato Hadizan na kwance ga karin ruwa ana yi mata ta kumbara sumtum tamkar zata fashe, a dakin da take 78 kwance ita kadai ce sai Inna Tambai zaune gefenta ta rike hannun Hadizan wanda ake yi mata karun ruwa, a can wata kwana Gwoggo Halima na zaune ta makure taci kuka har ta ji kukan babu dadi. Yaya Amina ta kama kafafun Hadiza ta rike tana salati tare da cewa "Allah me na yi maka zaka dauke min Hadiza, yarinya mai hakuri da nisan hankali? Ya Ubangiji Ka baiwa Hadiza lafiya ko na sami kafar gafara daga gare ka, domin na san tsakanin da da mahafi akwai hisabi ---" Halima tace, "Haba Amina, ki yi hakuri ki kwantar da hankalinki don Allah ki aje wa` annan maganganu cikin ranki in Allah Ya yarda Hadiza za ta warke, ga abinda aka fid da mata can muna jira ta farfado a nuna mata kafin aje a rufe." Amina ta yi kwal kwal tace, "Yanzu duk wannan wahalad da aka sha babu dan?" Gwoggo Halima ta
🏠